• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Daga dukkan alamu manyan arewa daga bangarorin rayuwa daban-daban, tun daga ‘yan siyasa jami’an tsaro, tsofaffin shugabanni, sarakuna da sauran masu fada a ji a yankin arewacin Nijeriya sun tabbatar da bukatar hada kai don yi wa lamarin matsalar tsaro da ta addabi sassan arewacin kasar nan taron dangi, ‘A Yi ta ta Kare’.

Wannan kudurin ya fito fili a taron da gamayyar kungiyoyin yankin rewacin ‘Coalition Of Northern Groups’(CNG) ta gabatar a Abuja ranar Labara 24 ga watan Janairu 2024.

  • AFCON 2023: An Fitar Da Jadawalin Zagaye Na 16
  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru

A jawabinsa, shugaban taron kuma tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ya bayyana cewa, in har ana saon cin galabar matsalar tsaron da ke addabar yankin arewa dole a fuskanci lamarin ta haryar taron dangi tare da amfani da dabaru da dama da suka hada da karfafa jami’an tsaronmu da inganta hanyoyoyin tattara bayanan sirri tsakanin jami’anm tsaro. Haka kuma zuba jari don bukasa bangaren ilimi da tattalin arziki tare da tsunduma sarakuna cikin tafiyar da kasa zai yi mana maganin matsalar tsaro daga tushe.

Ya kuma nemi a tabbatar da hadin kai a tsakanin rundunonin tsaro don su yi aiki tare, “Dole gwamanatocin jihoji da na tarayya su hada kai a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da masu garkwua da mutane, hadin kan su tare da tafiya tare shi ne zai tabbatar da nasarar da ake bukata a wannan tafiyar’’ in ji shi.

A nasa jawabin tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya dora laifin matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu a sassan Nijeriya a kan yadda aka siyasantar da lamarin tsaro, “Dole mu fuskanci harkar tsaro ba tare da la’akari siyasa ba in har muna son tabbatar da kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya a wannna lokacin’’, in ji shi.

Ya kuma bukaci a yi amfani da dabaru da dama wajen yaki da ta’addanci, “Ka da mu bayar da muhimmanci kawai ga amfani da karfi a yaki da muke yi da matsalar tsaro, ya kamata a yi amfani da dabarun rungumar ‘yan ta’addan da samar musu wasu bababen more rayuwa, domin yaki kawai ba zai kai mu ga samun tabbataccen zaman lafiya ba a Nijeriya.

Haka kuma taron ya samu halatar mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Sa’ad, inda a jawabinsa ya bayyana cewa, Sarakuna a fadin tarayyar Nijeriya a shirye suke don tafiya tare da dukkan wani yunkuri  na samar da zaman lafiya a sassan Nijeriya musamman arewacin Nijeriya. Ya yi alkawarin mika sakamakon matsayar da aka cimma a taron ga taron kungiyar sarakuna arewa da za a yi a watan Faibrairu don a tattauna tare da daukar matakin da ya kamata.

Ya ce, Sarakuna na da gudummawar da za su bayar kuma za su ci gaba da bayarwa wajen tabbatar da tsaron al’umma a arewa. Ya kuma yaba wa gamayyar kungiyoyin arewa a kan shiryan taron.

A nata tsokacin, Kungiyar Dattawan Arewa, a karkashin shugabancin Farfeasa Ango Abdullahi, ta nuna jin dadinta tare da yaba wa gamayyar kungiyoyin yankin arewa da suka samu shirya wannan taron da ya zama irinsa na farko a tarihin yankin arewa.

Jawabin haka ya fito ne daga bakin mai magana da yawun kungiyar, Kwamrade Abdul-Azees Suleiman, wanda ya ce, taron da ya hada masana daga bangarori da dama zai samar da mafita da mahukunta za su yi amfani da ita wajen samar wa yankin arewa maganin matsalar tsaron da ake fuskanta wanda ta haifar da nakasu ga tattalin arzikin kasa ya kuma ci rayukan al’umma da dama a ‘yan skekarun nan.

Ya kuma ce, taron ya samar da dandamalin da masana za su baje kolinsu a kan yadda za a kawo karshen mastalar tsaro a kasar na, a kan haka ya bukacu hukumomin gwamnatocin jihohi da na tarayya su rungumi matsayar da taron ya fitar don yin aiki da su, ta haka za a tabbatar da nasarar da ake bukata.

Da yake jawabin godiya ga maharta taron, daya daga cikin jagororin da suka shirya taron, Dakta Nastura Ashir Shariff ya bayyana yadda matsalar tsaro ta shafi dukkan bangaren rayuwar al’ummar Nijeriya musamman yankin arewa.

Ya kuma amince da shawarar cewa, yaki da mastalar tsaro na bukatar hadin kan dukkan bangarorin al’umma da kuma aiki tare a tsakanin gwamnatin jihohi da na tarayya har zuwa matakin kananan hukumomi,. Ya nemi hadin kai da kasashe makwabta domin ta haka za a iya dakile rikice-rikicen da ke tsallakowa daga waje zuwa cikin gida Nijeriya.

Nastura Ashir Shariff ya kuma nemi gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da talauci da tsadar rayuwa da al’umma ke fuskanta, ya ce, matsalar rashin aiki yi a tsakanin matasa yana taimakawa wajen yaudarar matasanmu su fada ayyukan ta’addanci.

Daga karshe ya nemi gwammati ta yi amfani da dukkan sakamakon da taron ya fitar don kawo karshen matsalar tsaro a yankin arewa. Taron ya samu halarta gwamnoni, sarakuna gargajiya, masana harkokin tsaro da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Munakisar Dauke Sassan CBN Da FAAN Daga Abuja Zuwa Legas…

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

Related

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

9 hours ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

18 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

2 days ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 
Da É—umi-É—uminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

3 days ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

'Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.