ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

by Bello Hamza
2 years ago
Arewa

LABARAI MASU NASABA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

Daga dukkan alamu manyan arewa daga bangarorin rayuwa daban-daban, tun daga ‘yan siyasa jami’an tsaro, tsofaffin shugabanni, sarakuna da sauran masu fada a ji a yankin arewacin Nijeriya sun tabbatar da bukatar hada kai don yi wa lamarin matsalar tsaro da ta addabi sassan arewacin kasar nan taron dangi, ‘A Yi ta ta Kare’.

Wannan kudurin ya fito fili a taron da gamayyar kungiyoyin yankin rewacin ‘Coalition Of Northern Groups’(CNG) ta gabatar a Abuja ranar Labara 24 ga watan Janairu 2024.

  • AFCON 2023: An Fitar Da Jadawalin Zagaye Na 16
  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru

A jawabinsa, shugaban taron kuma tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ya bayyana cewa, in har ana saon cin galabar matsalar tsaron da ke addabar yankin arewa dole a fuskanci lamarin ta haryar taron dangi tare da amfani da dabaru da dama da suka hada da karfafa jami’an tsaronmu da inganta hanyoyoyin tattara bayanan sirri tsakanin jami’anm tsaro. Haka kuma zuba jari don bukasa bangaren ilimi da tattalin arziki tare da tsunduma sarakuna cikin tafiyar da kasa zai yi mana maganin matsalar tsaro daga tushe.

Ya kuma nemi a tabbatar da hadin kai a tsakanin rundunonin tsaro don su yi aiki tare, “Dole gwamanatocin jihoji da na tarayya su hada kai a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da masu garkwua da mutane, hadin kan su tare da tafiya tare shi ne zai tabbatar da nasarar da ake bukata a wannan tafiyar’’ in ji shi.

A nasa jawabin tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya dora laifin matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu a sassan Nijeriya a kan yadda aka siyasantar da lamarin tsaro, “Dole mu fuskanci harkar tsaro ba tare da la’akari siyasa ba in har muna son tabbatar da kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya a wannna lokacin’’, in ji shi.

Ya kuma bukaci a yi amfani da dabaru da dama wajen yaki da ta’addanci, “Ka da mu bayar da muhimmanci kawai ga amfani da karfi a yaki da muke yi da matsalar tsaro, ya kamata a yi amfani da dabarun rungumar ‘yan ta’addan da samar musu wasu bababen more rayuwa, domin yaki kawai ba zai kai mu ga samun tabbataccen zaman lafiya ba a Nijeriya.

Haka kuma taron ya samu halatar mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Sa’ad, inda a jawabinsa ya bayyana cewa, Sarakuna a fadin tarayyar Nijeriya a shirye suke don tafiya tare da dukkan wani yunkuri  na samar da zaman lafiya a sassan Nijeriya musamman arewacin Nijeriya. Ya yi alkawarin mika sakamakon matsayar da aka cimma a taron ga taron kungiyar sarakuna arewa da za a yi a watan Faibrairu don a tattauna tare da daukar matakin da ya kamata.

Ya ce, Sarakuna na da gudummawar da za su bayar kuma za su ci gaba da bayarwa wajen tabbatar da tsaron al’umma a arewa. Ya kuma yaba wa gamayyar kungiyoyin arewa a kan shiryan taron.

A nata tsokacin, Kungiyar Dattawan Arewa, a karkashin shugabancin Farfeasa Ango Abdullahi, ta nuna jin dadinta tare da yaba wa gamayyar kungiyoyin yankin arewa da suka samu shirya wannan taron da ya zama irinsa na farko a tarihin yankin arewa.

Jawabin haka ya fito ne daga bakin mai magana da yawun kungiyar, Kwamrade Abdul-Azees Suleiman, wanda ya ce, taron da ya hada masana daga bangarori da dama zai samar da mafita da mahukunta za su yi amfani da ita wajen samar wa yankin arewa maganin matsalar tsaron da ake fuskanta wanda ta haifar da nakasu ga tattalin arzikin kasa ya kuma ci rayukan al’umma da dama a ‘yan skekarun nan.

Ya kuma ce, taron ya samar da dandamalin da masana za su baje kolinsu a kan yadda za a kawo karshen mastalar tsaro a kasar na, a kan haka ya bukacu hukumomin gwamnatocin jihohi da na tarayya su rungumi matsayar da taron ya fitar don yin aiki da su, ta haka za a tabbatar da nasarar da ake bukata.

Da yake jawabin godiya ga maharta taron, daya daga cikin jagororin da suka shirya taron, Dakta Nastura Ashir Shariff ya bayyana yadda matsalar tsaro ta shafi dukkan bangaren rayuwar al’ummar Nijeriya musamman yankin arewa.

Ya kuma amince da shawarar cewa, yaki da mastalar tsaro na bukatar hadin kan dukkan bangarorin al’umma da kuma aiki tare a tsakanin gwamnatin jihohi da na tarayya har zuwa matakin kananan hukumomi,. Ya nemi hadin kai da kasashe makwabta domin ta haka za a iya dakile rikice-rikicen da ke tsallakowa daga waje zuwa cikin gida Nijeriya.

Nastura Ashir Shariff ya kuma nemi gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da talauci da tsadar rayuwa da al’umma ke fuskanta, ya ce, matsalar rashin aiki yi a tsakanin matasa yana taimakawa wajen yaudarar matasanmu su fada ayyukan ta’addanci.

Daga karshe ya nemi gwammati ta yi amfani da dukkan sakamakon da taron ya fitar don kawo karshen matsalar tsaro a yankin arewa. Taron ya samu halarta gwamnoni, sarakuna gargajiya, masana harkokin tsaro da sauransu.

Arewa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
Manyan Labarai

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
Manyan Labarai

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

'Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.