ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

by Bello Hamza
2 years ago
Arewa

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Daga dukkan alamu manyan arewa daga bangarorin rayuwa daban-daban, tun daga ‘yan siyasa jami’an tsaro, tsofaffin shugabanni, sarakuna da sauran masu fada a ji a yankin arewacin Nijeriya sun tabbatar da bukatar hada kai don yi wa lamarin matsalar tsaro da ta addabi sassan arewacin kasar nan taron dangi, ‘A Yi ta ta Kare’.

Wannan kudurin ya fito fili a taron da gamayyar kungiyoyin yankin rewacin ‘Coalition Of Northern Groups’(CNG) ta gabatar a Abuja ranar Labara 24 ga watan Janairu 2024.

  • AFCON 2023: An Fitar Da Jadawalin Zagaye Na 16
  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru

A jawabinsa, shugaban taron kuma tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ya bayyana cewa, in har ana saon cin galabar matsalar tsaron da ke addabar yankin arewa dole a fuskanci lamarin ta haryar taron dangi tare da amfani da dabaru da dama da suka hada da karfafa jami’an tsaronmu da inganta hanyoyoyin tattara bayanan sirri tsakanin jami’anm tsaro. Haka kuma zuba jari don bukasa bangaren ilimi da tattalin arziki tare da tsunduma sarakuna cikin tafiyar da kasa zai yi mana maganin matsalar tsaro daga tushe.

Ya kuma nemi a tabbatar da hadin kai a tsakanin rundunonin tsaro don su yi aiki tare, “Dole gwamanatocin jihoji da na tarayya su hada kai a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da masu garkwua da mutane, hadin kan su tare da tafiya tare shi ne zai tabbatar da nasarar da ake bukata a wannan tafiyar’’ in ji shi.

A nasa jawabin tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya dora laifin matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu a sassan Nijeriya a kan yadda aka siyasantar da lamarin tsaro, “Dole mu fuskanci harkar tsaro ba tare da la’akari siyasa ba in har muna son tabbatar da kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya a wannna lokacin’’, in ji shi.

Ya kuma bukaci a yi amfani da dabaru da dama wajen yaki da ta’addanci, “Ka da mu bayar da muhimmanci kawai ga amfani da karfi a yaki da muke yi da matsalar tsaro, ya kamata a yi amfani da dabarun rungumar ‘yan ta’addan da samar musu wasu bababen more rayuwa, domin yaki kawai ba zai kai mu ga samun tabbataccen zaman lafiya ba a Nijeriya.

Haka kuma taron ya samu halatar mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Sa’ad, inda a jawabinsa ya bayyana cewa, Sarakuna a fadin tarayyar Nijeriya a shirye suke don tafiya tare da dukkan wani yunkuri  na samar da zaman lafiya a sassan Nijeriya musamman arewacin Nijeriya. Ya yi alkawarin mika sakamakon matsayar da aka cimma a taron ga taron kungiyar sarakuna arewa da za a yi a watan Faibrairu don a tattauna tare da daukar matakin da ya kamata.

Ya ce, Sarakuna na da gudummawar da za su bayar kuma za su ci gaba da bayarwa wajen tabbatar da tsaron al’umma a arewa. Ya kuma yaba wa gamayyar kungiyoyin arewa a kan shiryan taron.

A nata tsokacin, Kungiyar Dattawan Arewa, a karkashin shugabancin Farfeasa Ango Abdullahi, ta nuna jin dadinta tare da yaba wa gamayyar kungiyoyin yankin arewa da suka samu shirya wannan taron da ya zama irinsa na farko a tarihin yankin arewa.

Jawabin haka ya fito ne daga bakin mai magana da yawun kungiyar, Kwamrade Abdul-Azees Suleiman, wanda ya ce, taron da ya hada masana daga bangarori da dama zai samar da mafita da mahukunta za su yi amfani da ita wajen samar wa yankin arewa maganin matsalar tsaron da ake fuskanta wanda ta haifar da nakasu ga tattalin arzikin kasa ya kuma ci rayukan al’umma da dama a ‘yan skekarun nan.

Ya kuma ce, taron ya samar da dandamalin da masana za su baje kolinsu a kan yadda za a kawo karshen mastalar tsaro a kasar na, a kan haka ya bukacu hukumomin gwamnatocin jihohi da na tarayya su rungumi matsayar da taron ya fitar don yin aiki da su, ta haka za a tabbatar da nasarar da ake bukata.

Da yake jawabin godiya ga maharta taron, daya daga cikin jagororin da suka shirya taron, Dakta Nastura Ashir Shariff ya bayyana yadda matsalar tsaro ta shafi dukkan bangaren rayuwar al’ummar Nijeriya musamman yankin arewa.

Ya kuma amince da shawarar cewa, yaki da mastalar tsaro na bukatar hadin kan dukkan bangarorin al’umma da kuma aiki tare a tsakanin gwamnatin jihohi da na tarayya har zuwa matakin kananan hukumomi,. Ya nemi hadin kai da kasashe makwabta domin ta haka za a iya dakile rikice-rikicen da ke tsallakowa daga waje zuwa cikin gida Nijeriya.

Nastura Ashir Shariff ya kuma nemi gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da talauci da tsadar rayuwa da al’umma ke fuskanta, ya ce, matsalar rashin aiki yi a tsakanin matasa yana taimakawa wajen yaudarar matasanmu su fada ayyukan ta’addanci.

Daga karshe ya nemi gwammati ta yi amfani da dukkan sakamakon da taron ya fitar don kawo karshen matsalar tsaro a yankin arewa. Taron ya samu halarta gwamnoni, sarakuna gargajiya, masana harkokin tsaro da sauransu.

Arewa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

'Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.