• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yawaitar ayyukan garkuwa da mutane a cikin Babban Birnin Tarayya Abuja a ‘yan kwanakin nan da ma wasu sassan Nijeriya, lamarin da ya ta da hankalin al’umman kasa da firgitasu.

‘Yan Nijeriyan na kara shiga damuwa a yayin da suke yekuwar a tabbatar da an zakulo ‘yan ta’addan da kuma masu daukan nauyinsu a matsayi wani mataki na kawo karshen matsalolin garkuwa da mutane da neman kudin fansa.

  • Jami’an Tsaro Sun Yi Dirar Mikiya Gidan Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata

Tsohon dan majalisar dattawa, Sanata Shehu Sani ya shaida a shafinsa na D cewa, za a iya ganowa da samu wadanda suke amfana da makuden kudaden da jama’an kasa ke biya da sunan fansa a duk lokacin da aka sace musu wani nasu.

Ya nuna gayar takaicinsa kan ayyukan ‘yan ta’addan masu garkuwan da mutane da karban miliyoyin daruruwa a hannun jama’a, yayin da kuma suke kunsa musu damuwa da takaici hadi da bakin ciki a duk lokacin da suka sace wani ko wasu.

“Su masu garkuwan mafiya yawansu yara ne wasu ma ‘yan kasa da shekara ashirin. Babu wani alamar morewa ko jin dadi a tattare da su, hatta kayan da suke sanyawa ba za ka ga wani alamin kayan more rayuwa a tattare da su ba, duk kuwa da makuden kudaden da suke amsa a hannun jama’a.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

“Tambayar a nan shi ne, su waye ke amfana da makuden kudaden da wadannan masu garkuwa da mutanen ke amsa? Kuma su waye ke samar musu da makamai da suke samun damar gudanar da ayyukan ta’addanci da su?,” Sanatan ya tambaya.

Rahotonni sun zo a baya-bayan da tsohon dan majalisar wakilai, Hon. Sani Muhammad Takori ya yi zargin cewa, ayyukan ‘yan ta’adda a Jihar Zamfara na samun goyon baya daga wasu jiga-jigan mutane.

Kazalika, a baya-bayan nan in za a iya tunawa, gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang, ya fito balo-balo ya ce, jami’an tsaro sun san wadanda suke amfana da aikace-aikacen ta’addanci a jihar.

Da yake ganawa da wata gidan talabijin, gwamnan wanda ke maida bayani kan hare-haren baya-bayan nan a jihar da ya lakume rayukan mutum sama da 200, ya ce, su ma ‘yan ta’addan an san su.

“Abun da zan iya fada muku kan kashe-kashe da hare-haren Filato a baya-bayan nan tsagwaran ta’addanci ne.

“Na yi imanin masu daukan nauyin ‘yan ta’addan nan da masu cin gajiyar ta’addancin da masu dauke da makaman an sansu. Jami’an tsaro sun sansu, sun san maboyarsu. Wannan dalilin ne ya sa muka nace kan cewa dole ne hukumomin tsaro su yi aikinsu, su tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma,” ya shaida.

Wani masanin harkokin tsaro, Mista Akogwu John, ya nuna matukar mamakinsa kan yadda hukumomin tsaro da gwamnatin tarayya suka yi gum kan wannan ikirarin na gwamnan Filato.

Ya ce, “Gwamnan Filato ya fito baro-baro ya ce hukumomin tsaro sun san wadannan mutanen wadanda suke haifar da wannan matsalar a ko’ina. Ban ga labarin yadda hukumomin tsaro suka karyata wannan ikirarin ba. Kenan akwai kamshin gaskiya.

“Muna rayuwa a kasar da komai ana wasu da shi har da lamarin tsaro. Su waye wadannan jiga-jigai mutane masu karfin da ke daukan nauyin kashe-kashen mutanen da ba su ji ba su gani ba kuma me ya sa gwamnati ta yi gum da bakinta?” ya tambaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

Next Post

Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

8 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

9 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

10 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

14 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

16 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

17 hours ago
Next Post
Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.