• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Dawo Da Martabar PDP A Katsina — Kwamitin Riƙon Ƙwarya

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
PDP

Kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar adawa ta PDP wanda uwar jam’iyyar ta turo Jihar Katsina domin daidaita al’amurra, ya ce zai mayae da hankali kan abubuwa guda uku daga cikin har da haɗa kan ‘yan jam’iyyar domin shafe tasirin sauran jam’iyyu. 

Shugaban kwamitin rikon kwaryar, Alhaji Musa A. Karim, ya bayyana haka jim kadan bayan sun kammala taro da mambobin jam’iyyar.

  • Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman
  • Sanusi Ya Amince Da Mayar Da Wasu Ma’aikatun CBN Zuwa Legas

Ya ce bayan tattara hankalin ‘ya’yan jam’iyyar waje guda, za su tabbatar sun sasanta duk wani sabani da sauran bangarori da suka samu rashin fahimtar juna a baya.

“Muna da kalubale a wannan jam’iyya ta PDP a Katsina, amma hakan ba zai hana mu ba samun kwarin gwiwa wajen ganin mun dawo da martabarta a Jihar Katsina ba,” in ji shi.

Ya kara da cewa abu na uku da jam’iyya ke fuskanta shi ne zaben cike gurbi da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta gudanar a watan Fabrairu, 2024, wanda ya shafi dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Sabuwa da Kankara da kuma Faskari.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Idan za a yi tunawa dan takarar majalisar tarayya karkashin jam’iyar APC a zaben 2023, Honarabul Dalhatu Shehu Tafoki ya kai karar Hon. Jamilu Mohammed Lion, wanda INEC ta bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben.

Karim, ya ci gaba da cewa wannan kwamiti na rikon kwarya zai tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben da za a sake.

Kwamitin na mutum 15 da suka hada da Hon. Musa A. Karim shugaban jam’iyyar PDP da Hon Sanusi Ali da Hon. Abubakar Lawal da Hon. Abubakar Yusuf da Hon. Ibrahim Assalamu Alaikum da Hon. Nura Gambo da Hon. Tijjani Mashasha.

Sauran sun hada da Hon. Ubaida Jafar da Hon. Lawal Magaji Ɗanɓaci da Hon. Danjuma Altine da Hon. Haruna Garba, (Dogo na Maraya) da Hon. Ibrahim Tafashiya da Hon. Ubaida Mai’adua da Hon. Shitu Magami da kuma Halina Zubairu Ɗanbata a matsayin sakatariyar rikon kwarya ta jam’iyyar PDP a Katsina

Jam’iyyar PDP dai a Jihar Katsina na fama da rikicin da ya kai ta ga rashin nasarar zaɓe5n gwamnan da ya gabata tare rasa wasu kujerun ‘yan majalisar tarayya a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

PDP
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa 17 A Filato

'Yansandan Sun Ceto Mutane 14, Sun Kashe Dan Bindiga A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

PDP

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.