Mazauna yankin da ke kan hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina sun nuna rashin jin daɗi kan dakatar da aikin gyaran babbar hanyar, inda suka zargi Ibrahim Kabir Masari, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, da kuma Gwamna Dikko Umar Radda da hannu wajen soke kwangilar saboda dalilan siyasa.
Mutanen ƙauyuka irin su Birchi, da Burdugau, da Yargoje, da Tudu da Yantumaki sun bayyana cewa wannan mataki ya bar hanya cikin mummunan yanayi, duk da cewa ɗaya daga cikin hanyoyin da aka fi amfani da su a jihar Katsina. Aikin wanda ya kai kimanin ₦147.6 biliyan, an bai wa kamfanin Vipan Global Investment Resources Ltd kwangilar a watan Afrilu 2024 tare da amincewar Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC), kafin Ma’aikatar Aiyuka ta bayar da umarnin dakatar da aikin a watan Yuli bisa hujjar “rashin kuɗi.”
- Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
- Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Sai dai mazauna yankin sun yi watsi da wannan hujja, suna zargin Ministan Aiyuka, David Umahi, da bin umarnin Masari da Radda saboda suna ganin kamfanin yana da alaƙa da jam’iyyar adawa ta PDP. Wani matashi daga Yantumaki, Tanko Bello, ya ce, “Dole ne kowa ya zama ɗan jam’iyya mai mulki kafin a yi masa aiki? Dukkanmu ‘yan ƙasa ne masu cancantar samun kulawar gwamnati.”
Mazauna yankin sun kuma ce dakatar da aikin ya ƙara tsananta matsalar tsaro, ya takaita kasuwanci, tare da haifar da haɗura akai-akai. Sun yi gargadin cewa wannan lamarin zai iya rage farin jinin jam’iyyar APC a jihar Katsina kafin zaɓen 2027. “Wannan abu raini hankalin jama’a ne,” in ji wani ɗan ƙasa. “Zamu nuna rashin jin daɗinmu lokacin da ya dace.”
Sun roƙi Shugaba Bola Tinubu da ya sa baki don dawo da aikin, suna bayyana matakin a matsayin abin kunya da zai iya lalata martabar gwamnatinsa a idanun jama’a.














