• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Rana Continental Synergy da hadin guiwar gwamnatin tarayya, sun karrama jihar Bauchi a matsayin gwarzowar jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas ta shekarar 2024.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ne ya amshi lambar yabon a madadin jihar, a yayin babban taron liyafa ta bangaren iskar gas da mai na Nijeriya da ya gudana a Abuja, wanda kuma kamfanin Rana Continental Syngergy ta shirya da hadin guiwar masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas hadi da ma’aikatar albarkatun mai.

  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige
  • Xi Ya Mika Gaisuwar Bikin Bazara Ga Dukkan Sinawa

Bala Muhammad wanda ya jinjina da kokarin masu shirya taron wajen zabar jihar gami da karramata, ya sha alwashin hada kai da shugaban kasa Bola Tinubu domin cimma manufar gwamnatin tarayya na shawo kan matsalolin da suka yi wa bangaren tattalin arzikin kasa dabaibayi.

Da ya ke samun wakilcin kwamishinan albarkatun kasa na jihar Bauchi, Hon. Muhammad Maiwada Bello, gwamnan ya misalta taron a matsayin mai cike da tarihi ta yadda jihar ta lashe kambon jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas a 2024 a fadin kasar nan.

Ya ce, wannan nasarar da jihar ta samu bai rasa nasaba da tsare-tsare da kyawawan manufofin da suke akwai a bangaren mai da gas gami da saukaka harkokin kasuwanci musamman bayan gano Mai a kogin Kolmani da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Ya ce, hakan zai kara janyo hankalin masu sha’awar zuba hannun jari domin su zo jihar su zuba hannun jarinsu domin cigaban jihar da ma kasa baki daya.

Maiwada Bello, ya ce, gwamnan jihar Bauchi na aiki tukuru domin kyautata bangaren makamashi domin tabbatar da samar da damarmakin zuba jari da ayyukan yi ga matasa.

Ya kuma ce, lambar yabon zai kara musu kumaji da kokarin zage damtse wajen yin duk mai yiyuwa domin kunkasa bangarorin makamashi.

A nasa jawabin, karamin minista (Gas) a ma’aikatar albarkatun mai, Ekperikpe Ekpo, ya ce, jihar Bauchi ta nuna kwarin guiwar za ta yi abun a zo a gani a bangaren makamashi yayin da take kokarin samar da damarmaki da kere-kere a bangaren masana’antun mai da gas a Nijeriya.

Da ya ke samun wakilcin daraktan gas na ma’aikatar Misis Oluremi Komolafe, ta ce, lambar yabon ya cancanci jihar Bauchi lura da rawar da take takawa wajen kyautata harkokin mai da iskar gas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban TechnologyJihar BauchiTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Gas Ya Jefa Al’umma Cikin Duhu Da Matsaloli A Bangaren Lantarki A Nijeriya

Next Post

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

57 minutes ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

1 hour ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

3 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

5 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

8 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

8 hours ago
Next Post
Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.