• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Kamfanin Rana Continental Synergy da hadin guiwar gwamnatin tarayya, sun karrama jihar Bauchi a matsayin gwarzowar jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas ta shekarar 2024.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ne ya amshi lambar yabon a madadin jihar, a yayin babban taron liyafa ta bangaren iskar gas da mai na Nijeriya da ya gudana a Abuja, wanda kuma kamfanin Rana Continental Syngergy ta shirya da hadin guiwar masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas hadi da ma’aikatar albarkatun mai.

  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige
  • Xi Ya Mika Gaisuwar Bikin Bazara Ga Dukkan Sinawa

Bala Muhammad wanda ya jinjina da kokarin masu shirya taron wajen zabar jihar gami da karramata, ya sha alwashin hada kai da shugaban kasa Bola Tinubu domin cimma manufar gwamnatin tarayya na shawo kan matsalolin da suka yi wa bangaren tattalin arzikin kasa dabaibayi.

Da ya ke samun wakilcin kwamishinan albarkatun kasa na jihar Bauchi, Hon. Muhammad Maiwada Bello, gwamnan ya misalta taron a matsayin mai cike da tarihi ta yadda jihar ta lashe kambon jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas a 2024 a fadin kasar nan.

Ya ce, wannan nasarar da jihar ta samu bai rasa nasaba da tsare-tsare da kyawawan manufofin da suke akwai a bangaren mai da gas gami da saukaka harkokin kasuwanci musamman bayan gano Mai a kogin Kolmani da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Ya ce, hakan zai kara janyo hankalin masu sha’awar zuba hannun jari domin su zo jihar su zuba hannun jarinsu domin cigaban jihar da ma kasa baki daya.

Maiwada Bello, ya ce, gwamnan jihar Bauchi na aiki tukuru domin kyautata bangaren makamashi domin tabbatar da samar da damarmakin zuba jari da ayyukan yi ga matasa.

Ya kuma ce, lambar yabon zai kara musu kumaji da kokarin zage damtse wajen yin duk mai yiyuwa domin kunkasa bangarorin makamashi.

A nasa jawabin, karamin minista (Gas) a ma’aikatar albarkatun mai, Ekperikpe Ekpo, ya ce, jihar Bauchi ta nuna kwarin guiwar za ta yi abun a zo a gani a bangaren makamashi yayin da take kokarin samar da damarmaki da kere-kere a bangaren masana’antun mai da gas a Nijeriya.

Da ya ke samun wakilcin daraktan gas na ma’aikatar Misis Oluremi Komolafe, ta ce, lambar yabon ya cancanci jihar Bauchi lura da rawar da take takawa wajen kyautata harkokin mai da iskar gas.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.