• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Rana Continental Synergy da hadin guiwar gwamnatin tarayya, sun karrama jihar Bauchi a matsayin gwarzowar jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas ta shekarar 2024.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ne ya amshi lambar yabon a madadin jihar, a yayin babban taron liyafa ta bangaren iskar gas da mai na Nijeriya da ya gudana a Abuja, wanda kuma kamfanin Rana Continental Syngergy ta shirya da hadin guiwar masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas hadi da ma’aikatar albarkatun mai.

  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige
  • Xi Ya Mika Gaisuwar Bikin Bazara Ga Dukkan Sinawa

Bala Muhammad wanda ya jinjina da kokarin masu shirya taron wajen zabar jihar gami da karramata, ya sha alwashin hada kai da shugaban kasa Bola Tinubu domin cimma manufar gwamnatin tarayya na shawo kan matsalolin da suka yi wa bangaren tattalin arzikin kasa dabaibayi.

Da ya ke samun wakilcin kwamishinan albarkatun kasa na jihar Bauchi, Hon. Muhammad Maiwada Bello, gwamnan ya misalta taron a matsayin mai cike da tarihi ta yadda jihar ta lashe kambon jiha mai tasowa a bangaren mai da iskar gas a 2024 a fadin kasar nan.

Ya ce, wannan nasarar da jihar ta samu bai rasa nasaba da tsare-tsare da kyawawan manufofin da suke akwai a bangaren mai da gas gami da saukaka harkokin kasuwanci musamman bayan gano Mai a kogin Kolmani da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

Ya ce, hakan zai kara janyo hankalin masu sha’awar zuba hannun jari domin su zo jihar su zuba hannun jarinsu domin cigaban jihar da ma kasa baki daya.

Maiwada Bello, ya ce, gwamnan jihar Bauchi na aiki tukuru domin kyautata bangaren makamashi domin tabbatar da samar da damarmakin zuba jari da ayyukan yi ga matasa.

Ya kuma ce, lambar yabon zai kara musu kumaji da kokarin zage damtse wajen yin duk mai yiyuwa domin kunkasa bangarorin makamashi.

A nasa jawabin, karamin minista (Gas) a ma’aikatar albarkatun mai, Ekperikpe Ekpo, ya ce, jihar Bauchi ta nuna kwarin guiwar za ta yi abun a zo a gani a bangaren makamashi yayin da take kokarin samar da damarmaki da kere-kere a bangaren masana’antun mai da gas a Nijeriya.

Da ya ke samun wakilcin daraktan gas na ma’aikatar Misis Oluremi Komolafe, ta ce, lambar yabon ya cancanci jihar Bauchi lura da rawar da take takawa wajen kyautata harkokin mai da iskar gas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban TechnologyJihar BauchiTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Gas Ya Jefa Al’umma Cikin Duhu Da Matsaloli A Bangaren Lantarki A Nijeriya

Next Post

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Related

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

46 minutes ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 hour ago
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

15 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

16 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

16 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

17 hours ago
Next Post
Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru

LABARAI MASU NASABA

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.