• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane Lokacin Da Ta Zo Karbar Kudin Fansa A Taraba

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Sojoji

Dakarun rundunar soji ta 93 da ke karkashin rundunar sojin Nijeriya ta 6, sun yi nasarar cafke wata mata da ake zargi da garkuwa da mutane, lokacin da take kokarin karbar kudin fansar wani da aka yi garkuwa da shi a jihar Taraba.

Haka kuma rundunar ta damke wani dan bindiga da ya shahara wajen safarar makamai da alburusai, yana sayar da su ga masu aikata miyagun laifuka a jihar da sauran sassan Nijeriya.

  • Ina Da Labarin Sirri ‘Yan Bindiga Za su Kawo Mun Farmaki – Gwamna Dikko Raɗɗa
  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Kashe ‘Yan Sanda 2 A Katsina

Bincike ya gano matar da ake zargin mai suna, Janet Igohia, ta auri wani fitaccen mai aikata laifuka wanda shi ne shugaba na biyu bayan Marigayiya Hana Terwase, da sojoji su ka kashe a shekarun baya.

Da yake karin bayani ga manema labarai, Kakakin rundunar, Laftanar Oni Olubodunde, ya ce “sojojin da ke aiki da sahihan bayanan sirri kan ayyukan dillalan makamai, su su ka kama Joshua Dutse Idah, mai shekaru 45.

“Sojojin sun bi sawun sa, wanda hakan ya sa aka kama shi a garin Ibbi, lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa Kaduna, a wata karamar mota kirar Volkswagen Sharon, mai lamba Rivers SKN-390AA.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

“Da aka yi masa tambayoyi, ya amsa cewa zai je jihar Katsina ne domin kawo bindigogi kirar AK-47 wanda aka biya shi wani bangaren kudin Naira 300,000.

“Bayan binciken da suka yi masa kan motar, sojojin sun gano bindigar PK 1 da harsashi na musamman 399 mm da 7.62 da kuma mujallun AK-47 guda 3,” in ji Oni.

Haka kuma kakakin rundunar ya ce rundunar ta cafke Janet Igohia, da ake zargi da garkuwa da mutane mai shekaru 31, bayan ta karbi kudi naira miliyan daya da rabi (1.5), domin biyan kudin fansa ga wani da aka sace a yankin Chanchangi da ke karamar hukumar Takum.

Ya ce Janet Igohia, ta bayyana cewa “ta auri Voryor Gata wani fitaccen mai laifi kuma tsohon shugaba na biyu ga marigayi Gana Terwase.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
Kotu Ta Daure Dillalan Miyagun Kwayoyi 15 Shekara 168 A Gidan Yari A 2023 – Marwa

NDLEA Ta Kuduri Aniyar Fatattakar Masu Safarar Miyagun Kwayoyi – Marwa

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.