• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2024 Hajj: Karancin Maniyyata Ba Nijeriya Kadai Ya Shafa Ba – NAHCON

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
2024 Hajj: Karancin Maniyyata Ba Nijeriya Kadai Ya Shafa Ba – NAHCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Watakila Nijeriya ba za ta iya cike dukkan guraben kujerun aikin Hajji 95,000 da aka ware mata na aikin Hajjin bana ba saboda har yanzu maniyyata ko dai ba su fara biyan kudin ba ko kuma ba su kammala biya ba.

Faduwar darajar kudin Nijeriya, Naira, ya sanya kudin aikin Hajji ya kai Naira miliyan 4.9 ga maniyyatan bana daga mafi karancin Naira miliyan 4.5 da Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta tantance. A ci gaba da daidaita tsarin da ake yi na kayyade farashin canji, Naira ta zarce zuwa matsayi mafi karanci a ranar 30 ga Janairu, 2024 inda aka sayar da ita kan 1,413 kan kowace Dala a farashin gwamnati.

  • Sin Za Ta Kaddamar Da Gangamin Yayata Ci Gaban Mata
  • Tinubu Ya Gwangwaje ‘Yan Wasan Nijeriya Da Kyautar Filaye Da Gidaje Da Lambar MON Ta Kasa

A ranar 3 ga Fabrairu, Hukumar NAHCON ta ce an bukaci maniyyata aikin Hajjin bana daga jihohin Kudu da su biya Naira 4,899,000; wadanda suka fito daga jihohin Arewa, Naira 4,699,000, sai na Yola da Maiduguri, Naira 4,679,000.

An ruwaito cewa Litinin din da ta gabata ce wa’adin karshe wanda hukumar ta bayar da niyyar biyan kudi na karshe domin bai wa hukumar damar mika kudaden ga ma’aikata kafin wa’adin ranar 25 ga watan Fabrairu da masarautar Saudiyya ta kayyade.

Hukumar ta NAHCON ta ware jimillar guraben aikin Hajji 75,000 ga jahohi 36 da Babban Birnin Tarayya da kuma 20,000 ga masu gudanar da yawon bude ido.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ko da yake hukumar ba ta bayyana adadin maniyyatan da suka yi rijista kawo yanzu ba, binciken da Daily Trust ta gudanar ya nuna cewa har yanzu yawancin jihohin ba su cika rabin adadin guraben da aka ba su ba.

Mahajjata 2,600 ne suka biya a Kano

Kakakin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano (SPWB), Suleiman Dederi, ya shaida wa wakilinmu cewa, kujeru 2,600 ne kacal daga cikin 5,993 da aka ware wa jihar.

Sai dai ya bayyana fatansa na cewa adadin zai karu kafin cikar wa’adin da har yanzu da yawa ke ci gaba da yi

Dederi ya ce ya yi imanin cewa adadin za karu kafin ranar Litinin su biya kudi a bankuna.

Katsina

Daga cikin kujeru 4,300 da aka ware wa Jihar Katsina, “kadan ne ‘yan kasa sama da 2,000 da ake nufi suka kammala biya, kamar yadda hukumar alhazai ta jihar ta bayyana.

Adamawa

Hukumar SPWB ta Adamawa ta ce daga cikin kujeru 2,448 da aka ware wa jihar, 1,778 ne kawai aka biya.

Sakataren hukumar ya bayyana cewa, “Ya zuwa yanzu maniyyata 1,778 sun riga sun biya kudin aikin Hajjin, yayin da wasu ke ci gaba da kokarin hakan.

Neja

Kakakin Hukumar SPWB ta Neja Jibrin Usman Kodo ya shaida wa wakilinmu cewa a cikin kujeru 3,592 da aka ware wa jihar, maniyyata 2,806 ne kawai suka samu sun biya kudin ajiya.

“Alhazan Jihar Neja sun kasu kashi biyu ne, akwai wadanda suka biya kudin ajiya na farko na Naira miliyan 4.5. Ya zuwa ranar Litinin muna da maniyyata 286 da suka biya Naira miliyan 4.5, amma har yanzu ba su biya cikon Naira 199. 556,” in ji shi.

Edo

Daga cikin guraben aikin Hajji 412 da aka ware wa Jihar Edo, mahajjata 250 ne suka fara ba da kudin ajiya; yayin da 123 suka kammala biya. Shugaban Hukumar SPWB, Ibrahim Oyarekhua, ya ce NAHCON ta ware ma’aikata 412 ga Jihar Edo kuma kimanin maniyyata 250 ne suka yi ajiya kan Naira miliyan 4.5 na farko.

Kwara

Sakataren Zartarwa na Hukumar SPWB na Kwara, Abdulsalam Abdulkadir, ya ce sama da maniyyata 2,000 ne suka biya cikakken kudin aikin Hajji daga cikin kujeru 3,419 da aka ware wa jihar.

FCT

Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta FCT, ya ce kasa da maniyyata 2,500 ne ya zuwa yanzu suka biya kudin tafiya daga cikin 4,365 da aka ware wa yankin.

Gombe

Wani jami’in hukumar SPWB na Gombe ya shaida wa wakilinmu cewa daga cikin kujerun aikin Hajji 2,506 da aka ware wa jihar, 600 ne kawai suka kammala biyansu; yayin da sama da 1,000 suka ba da ajiya.

Legas

Kimanin rabin guraben aikin Hajji 3,576 da aka ware wa jihar Legas an biya su gaba daya, kamar yadda kakakin hukumar jin dadin alhazai ta jihar, Taofeek Lawal ya bayyana.

Kaduna

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na hukumar SPWB ta Kaduna Yunusa Mohammed Abdullahi ya shaida wa wakilinmu cewa sama da kujerun aikin Hajji 6,000 da aka bai wa jihar.

Yayin da ya zuwa yanzu ba a ba da adadin maniyyatan da suka kammala rijistar ba, ya ce 4,000

Bauchi

Kujeru 3,364 na aikin Hajji ne aka bai wa Jihar Bauchi domin gudanar da aikin Hajjin bana. Sakataren Zartarwa na SPWB Abdurrahman Ibrahim Idris, ya bayyana a watan Disamba cewa hukumar ta sayar da 1,700 daga cikin kujerun.

Da yake zantawa da Daily Trust a karshen makon da ya gabata, Kakakin Hukumar Muhammad Sani Yunusa ya ce adadin maniyyatan da za su yi aikin Hajji ya karu daga kujeru 1,700 .

“Amma ba zan iya bayar da ainihin adadin adadin maniyyatan da suka kammala biyan kudinsu na aikin Hajjin 2024 ba,” in ji shi.

Delta

Jami’in Kula Da Harkokin Addinin Musulunci na Jihar Delta, Sheikh Yahaya Ufuoma Mohammed, ya ce an ware wa jihar guraben gurabe 64.

Ya ce: “Kudin aikin Hajjin bana ya yi yawa. Don haka, a halin yanzu ba za mu iya bayyana adadin wadanda suka biya cikakken kudin ba.”

‘Tsarin kudin shiga zai hana Nijeriya cike gurbi’

Tsohon Shugaban Kungiyar ta TAFSAN Trabels and Tour, reshen kungiyar Nasrullahi-l-fatih Society (NASFAT), Maruf Arowosaye, ya ce da kudin da ake biya a halin yanzu ya yi yawa don haka zai yi wahala Nijeriya ta samu cike kujeru 95,000 da masarautar Masarautar Saudi Arabiya ta ware mata.

Da yake zantawa da Daily Trust, ya ce: “Ba wani abu da Allah ba zai iya yi ba, amma a zahiri zai yi wuya mu cika kason da aka bamu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Kayan Abinci Ya Ƙaru A Jihohin Nijeriya 36, Abuja, Kano, Borno Farashin Kaya Ya Sauka

Next Post

‘Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na’urar Zamani A Kebbi

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
Hajj
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
‘Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na’urar Zamani A Kebbi

'Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na'urar Zamani A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Hajj

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.