ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na’urar Zamani A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
'Yan sanda

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kebbi ta kaddamar da ofishin rajistar motoci ta na’urar zamani (CMR) domin yaki da masu aikata miyagun laifukan satar abin hawa.

Bukatar yin rajistar motocin na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafi’u Abubakar, inda aka raba wa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Farashin Kayan Abinci Ya Ƙaru A Jihohin Nijeriya 36, Abuja, Kano, Borno Farashin Kaya Ya Sauka
  • Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Kazalika takardar ta kara da cewa, “A bisa shirin babban sufeton ‘Yan sanda na 22, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, NPM, Ph.D, na inganta harkokin tsaro a cikin gida Nijeriya, rundunar ‘yansandan jihar Kebbi ta bayar da umarnin kaddamar da babban ofishin yin rigistar motocin ta na’urar zamani wato ‘Digitalized Central Motor vehicle Registry (CMR)’ da ke Hedikwatar Rundunar a Gwadangaji, da ke a Birnin Kebbi.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ta kara ta cewa an yi shi ne don magance laifukan da suka shafi abubuwan hawa da nufin inganta lafiyar jama’a da tsaron mutanen jihar Kebbi.

Takardar ta ci gaba da cewa, duba da yadda manyan laifukan da suka shafi motoci ke karuwa, rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta sake farfado da babban ofishin rajistar motoci ta hanyar sanya shi a cikin na’ura mai kwakwalwa ta yadda za a rika amfani da bayanan mota guda domin ya ba da hakikanin bayanai daga ’yansandan a yayin gudanar da bincike na zamani wajen kokawa da laifukan satar motoci a fadin jahohin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Har ilayau, kaddamar da ofishin rajista yana da fa’idodi masu yawa, waɗanda suka haɗa da; inganta tsaro da samun bayanai na kai-tsaye daga na’urar CMR ga ‘yan ƙasa, haka kuma za su iya samun babban kwarin gwiwa ga tsaron motocinsu.

Haka kuma ingantattun bayanan abin hawa za su taimaka wajen dakile wa da magance laifuka satar motoci cikin sauki, da nufin tabbatar da cewa, an kiyaye kadarorin ‘yan kasa.

Hakazalika, ‘Yan sandan za su kasance mafi kyawun kayan aiki don aiwatar da dokokin da suka shafi motoci, kamar rajista da lasisi. Hakan zai haifar da samar da ingantattun hanyoyi da inganta hanyoyin tafiyar da ababen hawa da za su amfanar da duk masu amfani da ababen hawansu a kan hanya.

Bugu da kari takardar ta ce cikakkun bayanai na motoci za su zama abin hana masu aikata laifuka waɗanda za su iya amfani da ababen hawa don ayyukan da ba su dace ba. Sanin cewa jami’an tsaro na da damar samun ingantattun bayanai na iya hana aikata laifukan satar motoci a jahohin kasar nan.

Don haka Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Kebbi, CP Chris Aimionowane, psc, mnips, ya bukaci al’ummar Jihar masu son zaman lafiya da su rungumi shirin na IGP na kawo sauyi ta hanyar yiwa motocinsu rajistar ta na’uran zamani da nufin bayar da gudunmawarsu tare da inganta tsaro na cikin gida da tabbatar da tsaro ga kowa da kowa.

Daga karshe don yin rijistar motar ku, ku ziyarci https://cmris.npf.gov.ng ko tuntuɓi Jami’in da ke kula da ofishin yin rigiata a rundunar ‘yansanda ta jihar akan wannan Lamba 08062118443 ko don neman karin bayani.

'Yan sanda
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.