• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakuri Shi Ne Babban Sirrin Samun Nasarar Kowacce Sana’a –Khadija Bello

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Hakuri Shi Ne Babban Sirrin Samun Nasarar Kowacce Sana’a –Khadija Bello
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

Khadija Bello matashiya ce da duk da lalurar rashin iya tafiya da ya same tun tana makarantar sakandire hakan bai hana ta cika burinta na samun nasara a harkokin kasuwancin da ta sa a gaba ba. Wakiliyarmu Amina Bello Hamza ta tattauna da ita, inda ta bayyana yadda ta fara sana’ar saka da kuma sayar da atamfa. Ga dai yadda tattaunawar ta kasance.

Da Farko Za Mu So Ki Bayyana Mana Sunanki?

Sunana Khadija Bello, ina zaune garin Samarun Zariya,  na yi karatu firamari da sakandari duk a Samarun Zariya.

Ko Malamar Nada Aure?

Ban yi aure ba ina zaune da iyayena ne

Wanne sana’a kike yi a halin yanzu?

Sana’a nake yi a yanzu shi ne sakar kayan sanyi sannan ina sayar da duk wani nau’i na sutura, kamar atamfa takalma, a takaice dai har kayan Lefe na aure muna hadawa

Menene Ya Baki Sha’awar Fara Wannan Sana’ar?

Ni tun da farko na tashi da son inga ina wani abu, saboda ko da yaushe ina zaune sai na nemi wani abu da zan rinka yi wanda zai dauke hankalina daga kan larurar da nake fama da ita (ina fama da lalurar rashin iya tafiya), tun da na tashi na ga mahaifiyata na saka sai nima na fara a hankali tun ban kai shekara goma ba nake sakar, A hankali kuma sai hankalina ya kai kan sutura, naga ina so in fara sai na nemi masu siyarwa suka ban shawara suka kara kwadaitamin har na ji Ina son sana’ar a raina sosai sannan na fara.

Idan Mutum Na Son Fara Wanna Sana’ar, Wani Abu Zai Tanada Don Samun Cikakkiyar Nasara?

Idan saka ne zaka tanaji kwarasshe da zare sannan ka mayar da hankali domin shi sakar yana son natsuwa, ta yadda in an nuna maka yau gobe za ta iya kwatantawa

Idan Kuma sayar da sutura ne kamar ni gaskiya nafi siyarwa a kafafen sadarwa na zamani ‘Social Media’ toh za ta bukaci wayar daukar hoto, sannan lokaci ta yadda idan me son siyan kaya ya yi magana za ta iya samun cikakken lokacin da za su yi ciniki har a kai ga aika musu da kayan.

Ta yaya kike tallata hajojinki?

Kinga ni Facebook na fi tallata hajata sai Whatsapp, idan zan yi tallar kayan nakan sa garin da nake sannan na sa number na ta yadda duk me bukata zai min magana inbod a Facebook (Deejah bint Bello) ko a kira number ta 0808403680 ko su yi min magana ta Whatsapp a number da na rubuta.

Ko kin taba samun tallafin gwamnati ko wata hukumar a harkar kasuwancinki?

Ban taba samu ba amma inda zan samu wani tallafi inaso, sai in bude babban shago in dauki ma’aikata wadanda za su ringa tayani kula da shagon, Ta yadda su ma za su samu abin yi.

Ko zaki bayyana mana wani abin da ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka a rayuwarki na wannan sana’ar?

Farin ciki kullum, alhamdulillah, amma akwai kayan lefen da na fara hadawa a rayuwata, ranar na yi farin ciki sosai domin abin da ban yi tsammani ba ne, kwatsam kuma sai ya zo gareni shi yasa har yau na kasa mantawa, na bakin ciki kam bawai babu ba ne, amma farin cikin yana danne shi, Alhamdulillah.

Wanne shawara kike da shi ga al’umma?

Shawarana shi ne su yi hakuri yanzu rayuwa ta yi tsada ba komi ake samu yadda ake so ba, sai an yi hakuri an jure za a ji dadi nan gaba, Duk wanda yake da damar karatu to su yi iya kokari suga sun yi karatunnan sosai, idan kuma sana’ar ne toh kar a sa sanya a yi sana’ar da gaske, Da yawa sukan kasa jurewa a kan abin da suke kai wasu kuma suna da gaggawa, suna so su fara yau kuma har a sansu a yau, a a hakan ba zai yiwu ba sai an yi hakuri an tafi a hankali.

Ya kike ganin yanayin tarbiya a wannan lokacin?

Tarbiyya yanzu sai iyaye sun dage da sa ido sannan su dage da addua duk wuya iyaye su yi kokari wajen sauke hakkin da ya hau kansu, A kula da karatunsu idan babu halin karatu a samu a koya musu sana’a domin rashin abin yi shi ne ke haifar da tabarbarewar tarbiyya idan yaro ba karatu ba abin yi hakan zai sa zuciyarsa ta gurbace har ta kaishi ga aikata wani abu mara kyau wadda iyaye ba za su ji dadi.

Ko kina da wani shawara ga al’umma?

Mu ci gaba da hakuri sannan in mun samu da sauki mu saukaka wa al’umm hakan zai kawo mana sauki da sauyi a rayuwarmu gaba daya, Allah yasa mu da ce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Gami Da Kashe Wani Lauya

Next Post

Wata Mata Ta Taba Zagina A Kan Littafina ‘Umarnin Uba’ —Yareema Shaheed

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

6 days ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

3 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Wata Mata Ta Taba Zagina A Kan Littafina ‘Umarnin Uba’ —Yareema Shaheed

Wata Mata Ta Taba Zagina A Kan Littafina ‘Umarnin Uba’ —Yareema Shaheed

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.