• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Afirka Ta Yi Maraba Da Sakon Xi Jinping Ga Taron AU Karo Na 37

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon taya murna ga taron kungiyar Tarayyar Afrika (AU) karo na 37 a ranar 17 ga wata, sakon da aka yi maraba da shi sosai a nahiyar.

Jama’a daga kasashen Afrika daban-daban na ganin cewa, sakon ya nuna yadda Sin ta dauki dangantakarta da Afrika da muhimmanci da kuma goyon baya mai karfi da take ba ci gaban nahiyar da farfadowarta.

  • Kasar Sin: Mutane Miliyan 474 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Hutun Bikin Bazara
  • Gwamnatin Katsina Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Aiwatar Da Dokar Hana Boye Hatsi Da Tsadar Haya

Sun kuma yi ammana cewa dangantakar bangarorin biyu za ta ci gaba da kasancewa tubalin hadin gwiwar kasashe masu tasowa da ma na hadin gwiwar Afrika da sauran kasashen duniya, haka kuma suna sa ran ganin bangarorin biyu sun samu ci gaba a tafarkin zamanantar da kansu. Tuni dai aka dauki matakai masu ruwa da tsaki wajen hada hannu domin gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya da samar da karin alfanu gare su.

A cewar Amadou Diop, dan kasar Senegal mai fashin baki kan harkokin da suka shafi kasar Sin, hadin gwiwar Sin da Afrika misali ne na hadin gwiwar kasashe masu tasowa wanda ke taka muhimmyar rawa a harkokin duniya. Ya ce hadin gwiwar Sin da Afrika na kunshe da sabon ra’ayin huldar kasa da kasa na moriyar juna, kuma ya samar da karin kuzari da karin damarmakin ci gaba ga duniya.

Shi kuwa Cavins Adhil, masanin harkokin kasa da kasa na kasar Kenya, ya ce tun bayan hadin gwiwar shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya, ababen more rayuwa a nahiyar Afrika sun samu ci gaban da ba a taba gani ba, lamarin da ya aza tubalin zamanantar da nahiyar da ma dunkulewarta. Ya ce shawarar raya duniya da ta tsaron duniya da ma ta jituwar mabambantan al’ummomi, wadanda kasar Sin ta gabatar, sun samu karbuwa a tsakanin kasashen Afrika. Ya ce al’ummar Sin da Afrika na da buri guda na samun ingantacciyar rayuwa. Kuma bisa la’akari da yanayinsu, Sin da Afrika za su yi aiki tare wajen samar da kyakkyawan muhallin cimma burikansu na ci gaba. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaCi gaban tattalin arzikin NijeriyaShugaban kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Biliyan 47: AEDC Ta Baiwa Fadar Shugaban Kasa Da Ma’aikatun Gwamnati Wa’adin Kwanaki 10

Next Post

Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana

Related

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

15 hours ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

16 hours ago
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
Daga Birnin Sin

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

17 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

18 hours ago
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

19 hours ago
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

21 hours ago
Next Post
Mbappe

Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.