• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Afirka Ta Yi Maraba Da Sakon Xi Jinping Ga Taron AU Karo Na 37

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon taya murna ga taron kungiyar Tarayyar Afrika (AU) karo na 37 a ranar 17 ga wata, sakon da aka yi maraba da shi sosai a nahiyar.

Jama’a daga kasashen Afrika daban-daban na ganin cewa, sakon ya nuna yadda Sin ta dauki dangantakarta da Afrika da muhimmanci da kuma goyon baya mai karfi da take ba ci gaban nahiyar da farfadowarta.

  • Kasar Sin: Mutane Miliyan 474 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Hutun Bikin Bazara
  • Gwamnatin Katsina Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Aiwatar Da Dokar Hana Boye Hatsi Da Tsadar Haya

Sun kuma yi ammana cewa dangantakar bangarorin biyu za ta ci gaba da kasancewa tubalin hadin gwiwar kasashe masu tasowa da ma na hadin gwiwar Afrika da sauran kasashen duniya, haka kuma suna sa ran ganin bangarorin biyu sun samu ci gaba a tafarkin zamanantar da kansu. Tuni dai aka dauki matakai masu ruwa da tsaki wajen hada hannu domin gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya da samar da karin alfanu gare su.

A cewar Amadou Diop, dan kasar Senegal mai fashin baki kan harkokin da suka shafi kasar Sin, hadin gwiwar Sin da Afrika misali ne na hadin gwiwar kasashe masu tasowa wanda ke taka muhimmyar rawa a harkokin duniya. Ya ce hadin gwiwar Sin da Afrika na kunshe da sabon ra’ayin huldar kasa da kasa na moriyar juna, kuma ya samar da karin kuzari da karin damarmakin ci gaba ga duniya.

Shi kuwa Cavins Adhil, masanin harkokin kasa da kasa na kasar Kenya, ya ce tun bayan hadin gwiwar shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya, ababen more rayuwa a nahiyar Afrika sun samu ci gaban da ba a taba gani ba, lamarin da ya aza tubalin zamanantar da nahiyar da ma dunkulewarta. Ya ce shawarar raya duniya da ta tsaron duniya da ma ta jituwar mabambantan al’ummomi, wadanda kasar Sin ta gabatar, sun samu karbuwa a tsakanin kasashen Afrika. Ya ce al’ummar Sin da Afrika na da buri guda na samun ingantacciyar rayuwa. Kuma bisa la’akari da yanayinsu, Sin da Afrika za su yi aiki tare wajen samar da kyakkyawan muhallin cimma burikansu na ci gaba. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaCi gaban tattalin arzikin NijeriyaShugaban kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Biliyan 47: AEDC Ta Baiwa Fadar Shugaban Kasa Da Ma’aikatun Gwamnati Wa’adin Kwanaki 10

Next Post

Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana

Related

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

11 hours ago
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana
Daga Birnin Sin

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

11 hours ago
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

13 hours ago
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

1 day ago
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
Daga Birnin Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

2 days ago
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

2 days ago
Next Post
Mbappe

Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.