• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi tir da karairayin da ake yadawa game da kisan kiyashi da kuma tilastawa mutane yin aiki a jihar Xinjiang, sannan ya yi kira da a yi kokarin kauce wa ra’ayin “tabka hasara” a yayin da yake amsa tambayoyi a taron tsaro na Munich a ranar Asabar.

Wang Yi ya ce, tun lokacin da aka kafa yankin Xinjiang na kabilar Uygur mai cin gashin kansa, yawan mutanen Uygur ya karu daga miliyan 3 zuwa sama da miliyan 12 ya zuwa yanzu. Kuma ana ba da kariya ga ‘yancin gudanar da addini na dukkan kabilu da ke wurin, inda ya ba da misali da cewa musulmai na da isasshen wuraren ibada kuma gwamnati ta dauki nauyin gyara da kula da masallatai.

  • Wang Yi: Sin Ta Sha Alwashin Zama Jigon Samar Da Daidaito A Duniya Mai Tangal-Tangal
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Kara Amfani Da Filaye Don Bunkasuwar Yankuna Mai Inganci

Da yake magana game da zargin da ake yi cewa ana tilastawa mutane yin aiki, Wang ya ce, yin amfani da wannan zargi a matsayin uzuri don shafawa kasar Sin bakin fenti, wata manufa ce ta kwace wa al’ummar Uygur ayyukan yi tare da hana su sayar da hajojinsu.

Ya kara da cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu cikin sauri ya haifar da rashin jin dadi da damuwa a tsakanin mahukuntan wasu kasashe, shi ya sa suke yada karairayi game da jihar Xinjiang don haifar da cikas, ta yadda za a hana ci gaban kasar Sin da farfado da tattalin arzikinta.

Bugu da kari, Wang Yi ya ce, ra’ayin da wasu ke da shi na “tabka hasara”, ba zabi ne da hankali zai dauka ba, kuma cin nasara tare shi ne makomar dan Adam.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Rahoton na shekara-shekara da aka fitar a Litinin din nan gabanin kammala taron tsaro na Munich, ya jaddada damuwar da ake da ita kan ra’ayin “tabka hasara”, yayin da ake samun karuwar tashe-tashen hankula a fannin siyasa da karuwar rashin tabbas na tattalin arziki.

A cewar rahoton, gwamnatoci da dama ba sa mai da hankali kan cikakkiyar fa’idar hadin gwiwar duniya, maimakon haka suna kara nuna damuwa cewa, suna samun moriya kasa da ta saura.

Wang ya ce, rahoton ya nuna yadda nahiyar Turai ke tunani da kuma damuwar da duniya ke ciki.

Ya bayyana cewa, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman bayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”. Yana mai cewa, kasashe da yawa sun fahimci cewa, tilas ne a kaucewa hasara.

Ya kara da cewa, ya kamata mu yi aiki tare, mu yi la’akari da muradun wasu tare da kare muradun kanmu, da inganta ci gaban hadin gwiwa tare da neman ci gaban kanmu, ta yadda za mu samu nasara tare, kuma nasara shi ne burin da ya kamata mu bi tare.

Wang ya ce, idan har ana son cimma nasara tare, kamata ya yi kasashe su zabi hadin kai kan rarrabuwar kawuna, hadin gwiwa kan sabani da bude kofa ga juna.

A ranar 18 ga watan Fabrairu ne aka kammala taron kwanaki uku na taron tsaro na Munich karo na 60 a birnin Munich na kasar Jamus. A yayin taron, mahalarta daga kasashe daban-daban sun tattauna batutuwa kamar rikicin Ukraine, rikicin Isra’ila da Falasdinu da kuma tsarin kasa da kasa. (Masu Fassarawa: Muhammed Yahaya, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihar XinjiangMinistan harkokin wajen sinZargin tauye hakkin dan Adam A Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana

Next Post

Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

Related

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

2 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

3 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

4 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

5 hours ago
Wang yi
Daga Birnin Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

6 hours ago
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000
Daga Birnin Sin

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

7 hours ago
Next Post
Murja

Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Wang yi

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.