ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Chad

Gwamnatin Chadi ta sanar da rufe iyakarta da Nijeriya nan take, tana mai cewa an ɗauki wannan mataki ne saboda dalilan tsaro, bayan rahotannin da ke cewa Amurka na shirin kai harin Soji a yankin Yammacin Afrika. Wannan mataki ya zo ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar damuwa a yankin Sahel.

Majiyoyin Soji a N’Djamena sun tabbatar a ranar Litinin cewa Shugaba Mahamat Idriss Déby Itno ya bayar da umarnin kulle iyakar ƙasar gaba ɗaya da Nijeriya, bayan samun bayanan sirri da suka nuna cewa wasu ƙungiyoyin ‘yan ta’adda daga arewacin Nijeriya na shirin tserewa zuwa cikin Chadi. An ce umarnin ya shafi manyan hanyoyin shiga da fita, musamman ta yankin tafkin Chadi.

  • Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
  • Za A Iya Samun Biliyoyin Daloli A Noman Zogale Da Kantu A Tekun Chadi

Rahotanni sun ce an sanya rundunar Sojin Chadi cikin shirin ko-ta-ƙwana, tare da tura dakaru da motocin yaƙi zuwa muhimman hanyoyin da ke haɗa ƙasashen biyu. Wannan mataki, in ji majiyoyi, yana nufin hana shige da fice ba bisa ƙa’ida ba da kuma kare yankunan kan iyaka daga barazanar ta’addanci.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa, Shugaba Déby ya ce gwamnati ba za ta yarda wata ƙungiya mai ɗauke da makamai ko wata ƙasa ta waje ta yi amfani da ƙasarsa wajen cimma wani buri ba. Ya ce, “Ba za mu bari wata ƙungiya ko wata ƙasa ta waje ta karya dokokinmu ko ta yi amfani da ƙasarmu don aikata wani abu da zai bar illa ga yankin ba.”

Masu lura da harkokin tsaro sun ce wannan mataki na iya yin tasiri ga hulɗar kasuwanci da zirga-zirga tsakanin kasashen biyu, musamman ga ƴan kasuwa da matafiya daga Borno, da Yobe da N’Djamena, inda ake yawan safarar kaya da abinci tsakanin ƙasashen.

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Chad
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya
  • Abubakar Sulaiman
    Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki
  • Abubakar Sulaiman
    Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin
Manyan Labarai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026
Next Post
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

LABARAI MASU NASABA

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.