• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Ta Ciri-tuta A Fannin Ingiza Ci Gaban Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar BRI Ta Ciri-tuta A Fannin Ingiza Ci Gaban Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masharhanta da yawa na yin tsokaci game da irin nasarorin da ake samu ta fuskar bunkasar ababen more rayuwa a sassan nahiyar Afirka, inda da yawa ke ganin shawarar nan ta “Ziri Daya Da Hanya Daya” ko BRI da Sin ta gabatar, na kan gaba wajen bunkasa ababen more rayuwa a kasashen Afirka, kuma shawarar ta kasance muhimmin jigo na bunkasa alakar zumunta dake tsakanin kasashen nahiyar da kasar Sin.

Wannan ma shi ne ra’ayin babban daraktan cibiyar nazarin manufofi da ba da shawarwari ta Afirka da Sin mista Paul Frimpong, wanda a baya bayan nan ya bayyana irin alfanun dake tattare da wannan shawara ta BRI, ta fuskar bunkasa ci gaban Afirka.

  • Xi Ya Sha Alwashin Hadin Gwiwa Da Shugaban Jamhuriyar Congo
  • Karo Na Farko Ne CIDCA Da Hukumar MDD Da Habasha Sun Sa Hannu Kan Takardar Hadin Gwiwa Da Ta Shafi Bangarori Uku

A cewar Frimpong, shawarar BRI na magance matsalolin da kasashen Afirka ke fuskanta a fannin samar da makamashi, da ruwa, da tsaftar muhalli, da fannonin sadarwa, da sufuri, da sauransu.

Ko shakka babu idan mun yi nazari ga kamalansu, da ma nasarorin da aka cimma na zahiri a fannin gina manyan ababen more rayuwa a Afirka, da bunkasar da nahiyar ke samu ta fuskar raya tattalin arziki, za mu ga cewa rungumar shawarar BRI da kasashen Afirka suka yi ya taimaka matuka wajen kaiwa ga nasarorin.

Tuni shawarar BRI ta taimakawa kasashen Afirka da dabarun bunkasa samar da ababen more rayuwa, ta yadda suke iya gudanar da hada hadar cinikayya tsakanin shiyyoyinsu, da ma sauran sassan duniya cikin sauki.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kaza lika samuwar ababen more rayuwa ya taimaka wajen rage tsadar gudanar da kasuwanci, da bunkasa takarar kasashen Afirka a cikin nahiyar da ma tsakanin su da sauran sassan kasa da kasa, wanda hakan ya haifar da nasarori a fannin raya tattalin arziki da ci gaba mai dorewa.

Wani abun lura ma shi ne yadda kasashen Afirka ke samun karin damar dunkulewa da sauran takwarorinsu, inda hakan ake fatan zai raya burin bunkasa cudanya, da cimma moriyar juna tsakanin kasashen nahiyar da ita kanta kasar Sin nan zuwa shekaru 50 masu zuwa. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Next Post

Sin Ta Samu Karuwar Kudaden Da Aka Kashe A Fannin Yin Sayayya A Lokacin Hutun Bikin Bazara

Related

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

58 minutes ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

2 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

3 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

20 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

21 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

22 hours ago
Next Post
Sin Ta Samu Karuwar Kudaden Da Aka Kashe A Fannin Yin Sayayya A Lokacin Hutun Bikin Bazara

Sin Ta Samu Karuwar Kudaden Da Aka Kashe A Fannin Yin Sayayya A Lokacin Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.