• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin makon nan ne  labarin fitar shararriyar ‘yar Tik-Tok dinnan wadda ake zargi da yawan kalaman batsa da rashin sanin ya kamata ta shiga hannun jami’an Hisbaar JIhar Kano bayan kwashe tsawon lokaci ana farautarta Bayan samun nasarar damke ta  ne kuma hukumar HIsba ta gurfanar da ita gaban kotun shari’ar musulunchi dake Kwana Hudu a yankin Karamar Hukumar Nasarawa inda kotun ta aike da ita gidan gyaran halin na Kurmawa har zuwa ranar 20 ga wtan feburairin shekara ta 2024 domin ci gaba da sauraron karar.

A cikin dakon zuwan wannan rana da kotu ta ayyana domin ci gaba da sauraron karar ta Murja Ibrahim Kunya, sai kwatsam labarin fitar ta daga gidan gyaran halin ya fantsama akafafen sada zumunta, wanda haka ya haifan da zafafan martini tare da zargin hannu wasu masu mulki ko masu hannu da shuni da ake ganin sune suka yi duk mai yiwuwa wajen satar hanyar fitar da Murjar, sannan kuma aka ci gaba da cece ku ce a kafafen sada zumuntar wanda hakan ne ya ja hankalin bangarorin daban daban da ake kallo suna da ruwa da tsaki cikin lamarin.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Tunda farko hukumar lura da gidajen gyaran hali na Jihar Kano ta bakin mai Magana da yawunta Musbahu Kofar Nasarawa Hukumar kula da gidajen ta musanta rahotanni cewa fitacciyar ‘yar Tik tok  Murja Ibrahim Kunya ta gudu daga gidan yari.

Musbahu K/Nasarawa cewa ya yi Wasu rahotanni  sun karade kafafen sada zumunta dake cewa Murja Kunya  wadda kotu ta aike da ita gidan ajiya ranar Larabar da ta gabata bisa zargin ta da ayyukan badala da bata tarbiyya a kafafen sada zumunta ta tsere daga gidan gyaran halin.

Ta cikin wani sakon murya da ya aikawa kafafen yada labarai, mai magana da yawun hukumar Musbahu Lawal Kofar Nasarawa, ya ce an saki Murja bisa beli kamar yadda doka ta tanada bayan samun takarda daga alkali.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Ya kara da cewa yamadidin da ake cewar ta gudu daga Gidan gyaran Halin  umarnin harbi ne akan duk wanda aka samu da  laifin guduwa daga gidan gyaran hali, kuma takarda ce ta tsare Murja sannan takarda ce ta sake ta. Inji Musbahu Gwamnatin Kano

An jawo hankalin gwamnatin jihar Kano kan zargin karya da ake ta yadawa a cikin al’umma musamman a kafafen sada zumunta na zamani  kan zargin sakin wata fitacciyar ‘yar TikTok mai suna Murja Ibrahim Kunya daga gidan gyaran hali bisa yada abun da bai dace ba cikin bidiyo sabanin tanadin dokokin da suka dace a  Jihar Kano.

A sanarwar da Kwamishinan yada labarai na Jihar Kano, Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu, yace Wannan zarge-zargen kwata-kwata ba su da tushe balle makama, ba gaskiya ba ne, rashin sanin ya kamata ne  kuma hasashe na wasu bata-gari da  masu rashin  kishin kasa da kishin Gwamnati da mutuncin Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf.

Idan dai ba a manta ba gwamnati ta san Murja Kunya ta gurfana a gaban wata Kotun Shari’a da ke Kwana Hudu a karamar Hukumar Nassarawa bisa zargin ta da yada wasu munanan faifan bidiyo a dandalin sada zumunta inda kotu ta bayar da umarnin tsare ta a gidan  gyaran hali kuma zuwa ranar Talata, 20 ga Fabrairu, 2023 bayan ta saurari bukatar neman belin ta. Sai dai ya zo ma Gwamnati cewa an sake samun wani sabon zarge-zargen da aka yi mata wanda ya sa jami’an tsaro suka fitar da ita domin bincike. Har yanzu dai shari’arta na ci gaba da wanzuwa kuma za ta ci gaba har zuwa matakin karshe da kotu ta yanke.

Don haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da zargin da ake yi wa Gwamnatin jihar Kano a matsayin ba komai bane illa kokarin bata mata suna  tare da tabbatar wa al’ummar jihar cewa za ta ci gaba da mutuntawa tare da kiyaye alfarmar abubuwan da aka tanadar a kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya. Inji Dantiye

A Halin yanzu haka Talatar Nan ne aka sake gabatar da Murja gaban kotu, Kuma tunda farar Safiya ita Murja ta halrci kotun, Kuma alkalin ya tambayi lauyanta inda ta amsa da cewar Yana hanya, Amma dai kotun tace ba zata jira zuwan lauyan nata ba, saboda haka sai kotun ta bada umarnin ga ma’aikatar Lafiya da akai Murja Asibitin domin bincika Kwakwalwar ta sannan ta bukaci Hukumar Hisba data ci gaba kulawa duk waniotsin Murja Ibrahim inda ta dage sauraron Shari’ar ta ta zuwa 20/5/2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

Next Post

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

45 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.