• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Labarai
0
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin makon nan ne  labarin fitar shararriyar ‘yar Tik-Tok dinnan wadda ake zargi da yawan kalaman batsa da rashin sanin ya kamata ta shiga hannun jami’an Hisbaar JIhar Kano bayan kwashe tsawon lokaci ana farautarta Bayan samun nasarar damke ta  ne kuma hukumar HIsba ta gurfanar da ita gaban kotun shari’ar musulunchi dake Kwana Hudu a yankin Karamar Hukumar Nasarawa inda kotun ta aike da ita gidan gyaran halin na Kurmawa har zuwa ranar 20 ga wtan feburairin shekara ta 2024 domin ci gaba da sauraron karar.

A cikin dakon zuwan wannan rana da kotu ta ayyana domin ci gaba da sauraron karar ta Murja Ibrahim Kunya, sai kwatsam labarin fitar ta daga gidan gyaran halin ya fantsama akafafen sada zumunta, wanda haka ya haifan da zafafan martini tare da zargin hannu wasu masu mulki ko masu hannu da shuni da ake ganin sune suka yi duk mai yiwuwa wajen satar hanyar fitar da Murjar, sannan kuma aka ci gaba da cece ku ce a kafafen sada zumuntar wanda hakan ne ya ja hankalin bangarorin daban daban da ake kallo suna da ruwa da tsaki cikin lamarin.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Tunda farko hukumar lura da gidajen gyaran hali na Jihar Kano ta bakin mai Magana da yawunta Musbahu Kofar Nasarawa Hukumar kula da gidajen ta musanta rahotanni cewa fitacciyar ‘yar Tik tok  Murja Ibrahim Kunya ta gudu daga gidan yari.

Musbahu K/Nasarawa cewa ya yi Wasu rahotanni  sun karade kafafen sada zumunta dake cewa Murja Kunya  wadda kotu ta aike da ita gidan ajiya ranar Larabar da ta gabata bisa zargin ta da ayyukan badala da bata tarbiyya a kafafen sada zumunta ta tsere daga gidan gyaran halin.

Ta cikin wani sakon murya da ya aikawa kafafen yada labarai, mai magana da yawun hukumar Musbahu Lawal Kofar Nasarawa, ya ce an saki Murja bisa beli kamar yadda doka ta tanada bayan samun takarda daga alkali.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Ya kara da cewa yamadidin da ake cewar ta gudu daga Gidan gyaran Halin  umarnin harbi ne akan duk wanda aka samu da  laifin guduwa daga gidan gyaran hali, kuma takarda ce ta tsare Murja sannan takarda ce ta sake ta. Inji Musbahu Gwamnatin Kano

An jawo hankalin gwamnatin jihar Kano kan zargin karya da ake ta yadawa a cikin al’umma musamman a kafafen sada zumunta na zamani  kan zargin sakin wata fitacciyar ‘yar TikTok mai suna Murja Ibrahim Kunya daga gidan gyaran hali bisa yada abun da bai dace ba cikin bidiyo sabanin tanadin dokokin da suka dace a  Jihar Kano.

A sanarwar da Kwamishinan yada labarai na Jihar Kano, Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu, yace Wannan zarge-zargen kwata-kwata ba su da tushe balle makama, ba gaskiya ba ne, rashin sanin ya kamata ne  kuma hasashe na wasu bata-gari da  masu rashin  kishin kasa da kishin Gwamnati da mutuncin Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf.

Idan dai ba a manta ba gwamnati ta san Murja Kunya ta gurfana a gaban wata Kotun Shari’a da ke Kwana Hudu a karamar Hukumar Nassarawa bisa zargin ta da yada wasu munanan faifan bidiyo a dandalin sada zumunta inda kotu ta bayar da umarnin tsare ta a gidan  gyaran hali kuma zuwa ranar Talata, 20 ga Fabrairu, 2023 bayan ta saurari bukatar neman belin ta. Sai dai ya zo ma Gwamnati cewa an sake samun wani sabon zarge-zargen da aka yi mata wanda ya sa jami’an tsaro suka fitar da ita domin bincike. Har yanzu dai shari’arta na ci gaba da wanzuwa kuma za ta ci gaba har zuwa matakin karshe da kotu ta yanke.

Don haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da zargin da ake yi wa Gwamnatin jihar Kano a matsayin ba komai bane illa kokarin bata mata suna  tare da tabbatar wa al’ummar jihar cewa za ta ci gaba da mutuntawa tare da kiyaye alfarmar abubuwan da aka tanadar a kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya. Inji Dantiye

A Halin yanzu haka Talatar Nan ne aka sake gabatar da Murja gaban kotu, Kuma tunda farar Safiya ita Murja ta halrci kotun, Kuma alkalin ya tambayi lauyanta inda ta amsa da cewar Yana hanya, Amma dai kotun tace ba zata jira zuwan lauyan nata ba, saboda haka sai kotun ta bada umarnin ga ma’aikatar Lafiya da akai Murja Asibitin domin bincika Kwakwalwar ta sannan ta bukaci Hukumar Hisba data ci gaba kulawa duk waniotsin Murja Ibrahim inda ta dage sauraron Shari’ar ta ta zuwa 20/5/2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

Next Post

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

35 seconds ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

1 hour ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

2 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

3 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

15 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

15 hours ago
Next Post
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.