• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Hukumar Sufuri ta Jihar Zamfara ta kama manyan motoci 50 da ke jigilar kayan abinci daga kasar nan za su shiga Jamhuriyar Nijar.

Hukumar, wacce ke aiwatar da umarnin shugaban kasa da ke da nufin kawo karshen matsalar karancin abinci da tara kaya, ta hana motocin da ke cike da hatsi iri-iri fita daga kasar.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Ina Iya Kera Na’urorin Da Suka Fi Na Kasashen Waje Inganci, In ji Adam

Idan ba a manta ba a ranar Alhamis din da ta gabata Shugaban Kasa Bola Tinubu ya umurci manyan jami’ai uku da suka hada da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro Nuhu Ribadu, da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Kayode Egbetokun da kuma Babban Daraktan Ma’aikatar Harkokin Gwamnati Yusuf Bichi da su hada kai da gwamnonin jahohi domin ganin an dakile mummunar dabi’ar nan boye kayan abinci.

An dauki matakin ne a yayin ganawar da shugaban kasar ya yi da gwamnonin a Abuja kan matsalar karancin abinci da ake fama da ita a halin yanzu sakamakon hauhawar farashin man fetur bayan cire tallafi da kuma rashin isasshiyar noma saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

A ranar Lahadin da ta gabata ne Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta ce ta dakatar da tireloli 15 da ke jigilar kayan abinci ta kan iyakokin Sokoto zuwa Jamhuriyar Nijar.

Kazalika, gwamnatin Jihar Kano ta rufe rumfunan ajiya guda 10 da aka ce suna tara kayan abinci.

Da yake tabbatar da kama manyan motocin guda 50 a Zamfara, Shehu Sani, dan asalin garin Zurmi da ke Karamar Hukumar Zurmi a jihar, ya shaida wa wani wakilinmu ta wayar tarho a ranar Litinin da ta gabata cewa, an tare motocin ne a Kauyen Gidan Jaja, kusa da garin. Wanda ke kan iyakar Nieriya da Jamhuriyar Nijar.

Kakakin ZARTO, Sale Shinkafi, ya yi zargin cewa manyan motocin na yunkurin safarar kayayyakin abinci ne zuwa Jamhuriyar Nijar.

Ya ce, “Mutanenmu sun tare motoci 50 makil da hatsi iri-iri a lokacin da suke kokarin fitar da su daga kasar. Mun umurci masu su koma su sayar wa ‘yan Nijeriya kayayyakin a kan farashin da ya dace.”

Shinkafi ya bayyana cewa motocin ba su da rakiyar jami’an hukumar amma an umurce su ne kawai su koma yankunansu su sayar da kayayyakin a farashi mai sauki.

Ya ce, “Kun san cewa babban abin da ke damunmu shi ne mu tabbatar da cewa ba a fitar da kayan abinci daga kasar nan ta barauniyar hanya ba. Mun ki ba su damar shiga Jamhuriyar Nijar ne kawai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Next Post

An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

5 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

5 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

13 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

13 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

16 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

16 hours ago
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.