• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
NEMA Ta Musanta Mallakar Wani Rumbun Ajiyar Abinci Da Aka Wawashe A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shehin Malami kuma babban masani a bangaren tattalin arziki (Economy), Farfesa Ahmad Sanda, da ke aiki a jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sokoto a tsangayar koyar da nazarin tattalin arziki, ya shaida cewar, matsalar da matasa ke haifarwa ta zuwa rumbunan adana kayan abinci da fasawa domin kwashewa ko daka wasoso ga mo-tocin dakon kayan abinci ba za su shawo kan matsalolin matsin rayuwa da ake ciki ba illa ma kara jefa kasar cikin mayuwacin hali.

Ya shaida cewar, ana cikin mawuyacin halin da akwai bukatar gwamnatoci da masu ruwa da tsaki za su tashi tsaye domin jawo hankalin matasa da su kauce wa dabi’ar fasa wurare da sunan neman abinci.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

A cewarsa: “Wannan alama ce ta kamarin yunwa da tsadar rayuwa da ake ciki. Hanya mafi sauki ta shawo kan wannan matsalar shi ne gwamnati ta tabbatar duk wani kayan abinci da aka ware domin rabarwa a irin wannan yanayin ana kawowa a rabar ba wai a je a tara a ajiye a rumbu ba.

“Domin kwasan kayan abinci a kai rumbunan ajiye abinci mutane za su yi tunanin an ajiye ne domin a yi sama da fadi da su. In so samu ne daga inda aka kawo abinci domin rabarwa kawai a kai su ga jama’a kai tsaye a tabbatar an rabar. Kai tun kafin ma su iso a yi tsarin da suka dace suna zuwa a mika ga jama’a. A irin lokacin da talakawa ke matsin rayuwa gaskiya babu bukatar zuwa a ajiye abinci a boye.”

A cewarsa, akwai bukatar a tsaurara matakan tsaro domin fasa wuraren adana kayan abinci wata alama ce da ke nuni da cewa an tura mutane zuwa bango, don haka idan ba a dauki matakan tsaro ba, nan gaba sai an rasa wurin da za a ajiye wani abu da sunan abinci, “A daidai gabar daukan matakin tsaro gwamnati ta tabbatar tana raba wa jama’a abinci ba zuwa a boye ba.”

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Dangane da masu daka wasoso kan kayan abinci a motocin dakon ‘yan kasuwa, bab-ban malamin ya ce, akwai fa babban matsala, yana mai cewa hakan ba zai yi komai ba illa kara jefa farashin kayayyaki domin ya yi tsada.

“Gaskiya wadannan matsalolin sun shafi wasu abubuwa da suka ma zarce sashin tat-talin arziki shi kadai. Domin babu wani bangare a bangaren tattalin arziki da ya bai wa jama’a damar daka wawa kan kayan mutane.

“Akwai bukatar masu ruwa da tsaki daga bangarori daban-daban su shigo cikin wan-nan matsalar, malamai su wayar da kai.

“Eh an sani idan mutane na cikin matsatsin rayuwa, mutane ba za su saurari wasu bayanan ba, amma ya kamata dukkanin masu ruwa da tsaki kowa ya fito ya tofa al-barkacin bakinsa da kuma yin abun da ya dace.

“Kuma yana da kyau a nusar da matasa illolin fasa kayan abincin mutane. Domin idan ana fasa kayayyakin mutane ba ma na gwamnati kadai ba har da na ‘yan kasuwa ka ga wannan ba cigaba zai kawo ba zai kara tabarbara tattalin arziki ne. domin hauhawar farashin kayayyaki da gwamnati ke kokarin ta ga ta shawo kansa abun zai ta’azzara.”

“Gwamnoni, shugabannin kananan malamai, limamai, fastoci, kungiyoyi, kowa da kowa da su fito su jawo hankalin matasa kan cewa daka wawa ga kayan jama’a ba shi ne mafita ga wannan matsalar ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba. Don a maima-kon a samu sassaucin kayayyaki to wasoso zai sa farashi ya kara yin sama ne.

“Domin dan kasuwa ya sayo kayansa ya yi asararsu ka ga ba zai koma ba hakan zai sanya a samu karancin kayayyakin da har farashi zai kara hauhawa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukunce-hukuncen Ganin Watan Ramadan

Next Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Related

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

48 minutes ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

3 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

4 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

5 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

6 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.