ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Rumbunan hatsi

Shehin Malami kuma babban masani a bangaren tattalin arziki (Economy), Farfesa Ahmad Sanda, da ke aiki a jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sokoto a tsangayar koyar da nazarin tattalin arziki, ya shaida cewar, matsalar da matasa ke haifarwa ta zuwa rumbunan adana kayan abinci da fasawa domin kwashewa ko daka wasoso ga mo-tocin dakon kayan abinci ba za su shawo kan matsalolin matsin rayuwa da ake ciki ba illa ma kara jefa kasar cikin mayuwacin hali.

Ya shaida cewar, ana cikin mawuyacin halin da akwai bukatar gwamnatoci da masu ruwa da tsaki za su tashi tsaye domin jawo hankalin matasa da su kauce wa dabi’ar fasa wurare da sunan neman abinci.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

A cewarsa: “Wannan alama ce ta kamarin yunwa da tsadar rayuwa da ake ciki. Hanya mafi sauki ta shawo kan wannan matsalar shi ne gwamnati ta tabbatar duk wani kayan abinci da aka ware domin rabarwa a irin wannan yanayin ana kawowa a rabar ba wai a je a tara a ajiye a rumbu ba.

ADVERTISEMENT

“Domin kwasan kayan abinci a kai rumbunan ajiye abinci mutane za su yi tunanin an ajiye ne domin a yi sama da fadi da su. In so samu ne daga inda aka kawo abinci domin rabarwa kawai a kai su ga jama’a kai tsaye a tabbatar an rabar. Kai tun kafin ma su iso a yi tsarin da suka dace suna zuwa a mika ga jama’a. A irin lokacin da talakawa ke matsin rayuwa gaskiya babu bukatar zuwa a ajiye abinci a boye.”

A cewarsa, akwai bukatar a tsaurara matakan tsaro domin fasa wuraren adana kayan abinci wata alama ce da ke nuni da cewa an tura mutane zuwa bango, don haka idan ba a dauki matakan tsaro ba, nan gaba sai an rasa wurin da za a ajiye wani abu da sunan abinci, “A daidai gabar daukan matakin tsaro gwamnati ta tabbatar tana raba wa jama’a abinci ba zuwa a boye ba.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Dangane da masu daka wasoso kan kayan abinci a motocin dakon ‘yan kasuwa, bab-ban malamin ya ce, akwai fa babban matsala, yana mai cewa hakan ba zai yi komai ba illa kara jefa farashin kayayyaki domin ya yi tsada.

“Gaskiya wadannan matsalolin sun shafi wasu abubuwa da suka ma zarce sashin tat-talin arziki shi kadai. Domin babu wani bangare a bangaren tattalin arziki da ya bai wa jama’a damar daka wawa kan kayan mutane.

“Akwai bukatar masu ruwa da tsaki daga bangarori daban-daban su shigo cikin wan-nan matsalar, malamai su wayar da kai.

“Eh an sani idan mutane na cikin matsatsin rayuwa, mutane ba za su saurari wasu bayanan ba, amma ya kamata dukkanin masu ruwa da tsaki kowa ya fito ya tofa al-barkacin bakinsa da kuma yin abun da ya dace.

“Kuma yana da kyau a nusar da matasa illolin fasa kayan abincin mutane. Domin idan ana fasa kayayyakin mutane ba ma na gwamnati kadai ba har da na ‘yan kasuwa ka ga wannan ba cigaba zai kawo ba zai kara tabarbara tattalin arziki ne. domin hauhawar farashin kayayyaki da gwamnati ke kokarin ta ga ta shawo kansa abun zai ta’azzara.”

“Gwamnoni, shugabannin kananan malamai, limamai, fastoci, kungiyoyi, kowa da kowa da su fito su jawo hankalin matasa kan cewa daka wawa ga kayan jama’a ba shi ne mafita ga wannan matsalar ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba. Don a maima-kon a samu sassaucin kayayyaki to wasoso zai sa farashi ya kara yin sama ne.

“Domin dan kasuwa ya sayo kayansa ya yi asararsu ka ga ba zai koma ba hakan zai sanya a samu karancin kayayyakin da har farashi zai kara hauhawa.”

Rumbunan hatsi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.