Kungiyar kwallon kafa ta Liverpool za ta karbi bakuncin takwararta ta Manchester City a filin wasa na Anfield, a wasan mako na 28 na gasar Firimiya Lig ta bana.
Dukkan kungiyoyin suna taka rawar gani a kakar wasa ta bana, inda Liverpool ke matsayi na biyu a kan teburin Firimiya, yayin da Manchester City ke bimata a matsayi na uku.
- Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Manchester United Da Manchester City
- Liverpool Ta Lashe Kofin Carabao Karo Na 10 Bayan Doke Chelsea A Wembley
A cikin Liverpool da Manchester City duk wadda ta samu nasara za ta dare kan teburin gasar Firimiya wanda Arsenal ke jagoranta a halin yanzu bayan doke Brentford a yammacin jiya Asabar.
Har yanzu Liverpool na fama da rauni a tsakanin yan wasanta, inda mai tsaron ragarta Alison Becker, Joel Matip, Diogo Jota da Thiago Alcantara duk suke fama da raunuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp