• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: ‘Yan Kasuwa Sun Koka Kan Samun Ƙarancin Ciniki A Kano

by Muhammad
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Farashin Kayan Abinci Ya Ƙaru A Jihohin Nijeriya 36, Abuja, Kano, Borno Farashin Kaya Ya Sauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da aka shiga watan Ramadan mai alfarma, ‘yan kasuwa a Kano na ci gaba da kokawa kan rashin samun kwastomomi don yin sayayyar kayayyaki.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar da suka zanta da manema labarai ranar Lahadi a Kano, sun danganta lamarin da karancin samun kwastomomi.

  • Ramadan: Tinubu Ya Buƙaci Mawadata Da Su Taimakawa Mabuƙata
  • An Kaddamar Da Kasuwar Baje Kolin Watan Ramadan A Kano

Wani mai sayar da kayan abinci, Malam Tanko Idris, ya ce idan aka kwatanta da shekarun baya, cin kasuwa ya ragu a bana.

Idris ya ce duk da cewa farashin wasu kayayyaki, musamman kayan masarufi yakan yi tashin gwauron zabi a lokacin azumin watan Ramadan, amma har yanzu mutane sukan yi sayayyar kayan.

Shi ma wani dan kasuwa mai suna, Saminu Dauda, ​​ya koka da yadda harkokin kasuwanci ba sa tafiya sosai kamar a baya.

Labarai Masu Nasaba

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

Ya bayyana cewa tabarbarewar tattalin arziki a kasar ya taimaka wajen samun kai a wannan yanayi.

Wani mai sayar da kayan lambu, Sani Ali, ya koka kan cewa lamarin ya ba shi mamaki idan aka kwatanta da abin da ya saba gani a kasuwa a duk lokacin da watan Ramadan ke gabatowa ko kuma ya fara.

Ali ya ce kwastomomi da dama sun koka da karancin kudade saboda yanayin tattalin arziki.

Ya kuma koka da yadda yanayin tattalin arziki ya shafi ciniki da kwastomomi da dama.

Wani kwastoma, Nura Baba, ya koka da tsadar shinkafa da gero da fulawa da kuma sukari, wanda a cewarsa ya ce abun yana damunsa musanman a lokacin azumi.

“Misali, ana sayar da sukari sama da Naira 5,5000 kan kowanne mudu, shinkafa ana sayar da ita sama da Naira 3,500, ana sayar da gero kan Naira 1,800 kan kowane mudu, da farashin kwai kan Naira 3,300, ta yaya suke so mu ciyar da azumin Ramadan?”

Ya kuma yi kira ga ‘yan kasuwa da ma su sayar da kayan abinci a jihar da su rage farashinsu a cikin wata mai alfarma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan KasuwakanoKayan AbinciRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙudurin Tinubu Na Samar Da Abinci Ba Faɗe A Fatar Baki Ba Ne Kaɗai, Gaskiya Ne – Minista

Next Post

Ramadan: ‘Yansandan Kano Sun Buƙaci Jama’a Da Su Ba Jami’an Tsaro Haɗin-kai

Related

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

2 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

3 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

11 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

15 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

21 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

1 day ago
Next Post
Ramadan: ‘Yansandan Kano Sun Buƙaci Jama’a Da Su Ba Jami’an Tsaro Haɗin-kai

Ramadan: 'Yansandan Kano Sun Buƙaci Jama'a Da Su Ba Jami'an Tsaro Haɗin-kai

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.