ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
AGOA

Dokar tabbatar da karuwar tattalin arziki da damar raya nahiyar Afirka (AGOA) muhimmiyar doka ce ta kasar Amurka, a fannin samar da gatancin ciniki ga kasashen Afirka. Kana an dade ana kallonta a matsayin tushen huldar Afirka da Amurka ta fuskar tattalin arziki. Amma a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata, wa’adin dokar ya cika, ko da yake dimbin kasashen dake nahiyar Afirka sun yi ta kira da a tsawaita wa’adin dokar. Wannan batu ya nuna ra’ayin kasar Amurka dangane da kasashen Afirka, wato ko-in-kula.

 

A shekarar 2000, gwamnatin Bill Clinton ta sa aka zartas da dokar AGOA da zummar zurfafa alakar ciniki tsakanin kasar Amurka da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara. Wannan doka ta shafi kasashe 32, inda aka ba su damar fitar da nau’ikan kayayyaki fiye da dubu daya zuwa kasar Amurka. Sa’an nan a shekarar 2023, wato shekara ta karshe da ake iya samun alkaluma masu nasaba da dokar, kasashen Afirka sun fitar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 9.7 zuwa kasar Amurka, bisa sharadin gatanci da aka tanada cikin dokar AGOA.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulkin kasar Amurka a farkon bana, yanayi ya sauya: An fara karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin kasashen Afirka da ake shigar da su kasar Amurka, da rufe hukumar samar da agaji a duniya ta kasar Amurka ta USAID, gami da barin wa’adin dokar AGOA ta cika ba tare da tsawaita shi ba a wannan karo. A hannu daya, kasar Amurka ta janye gatanci da tallafin da ta ba kasashen Afirka a baya, kana a dayan hannun, tana neman samun karin kudi daga wajensu, hakan ya kara raunana ayyukan masana’antun Afirka wanda ko da ma ba su da karfi. Bisa gargadin da hukumar kula da ciniki da ci gaban tattalin arziki ta Majalisar Dinkin Duniya (UNCTAD) ta gabatar a kwanan baya, rashin aikin dokar AGOA zai haddasa raguwar kayayyakin da ake fitar da su daga kasashen Afirka zuwa kasar Amurka sosai, musamman ma a kasashen Kenya, da Tanzania, da Madagascar, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

 

Yanzu haka, wasu shugabannin kasashen Afirka na kokarin lallashin masu fada-a-ji na kasar Amurka don su taimaka wajen tabbatar da tsawaitar wa’adin dokar AGOA. Kana wani jami’in fadar White House ta kasar Amurka shi ma ya ce akwai yiwuwar kara wa’adin da shekara daya. Sai dai karin harajin fito da kasar Amurka ta saka ma kayayyakin dimbin kasashen dake nahiyar Afirka ya riga ya kawar da ma’anar gatancin da dokar AGOA ta kunsa. Ban da haka ana shakku kan ko gwamnatin Trump na da sahihanci wajen tsawaita wa’adin dokar AGOA. A cewar Farhana Paruk, masaniyar ilimin al’amuran kasa da kasa ta kasar Afirka ta Kudu, gwamnatin Trump ka iya amfani da batun wajen matsawa kasashen Afirka lamba, don neman biyan bukatarta ta fuskar harkokin siyasa.

 

A zahiri, ra’ayin gwamnatin kasar Amurka na yanzu dangane da kasashen Afirka, ya kara zama na ko-in-kula, idan an kwatanta shi da na gwamnatin kasar na lokacin baya. Dalilin da ya sa ake samun wannan sauyi, shi ne raguwar karfin kasar Amurka, da tasirinta a duniya. A baya, kasar dake da imani kan makomarta ta iya samar da moriya ga sauran kasashe, don musayar goyon bayansu. Amma a zamanin yanzu, kasar Amurka tana kallon sauran kasashe a matsayin “masu samar mata da jini”, inda take lura da moriya ta gajeren lokaci kawai, maimakon adalci da abokantaka. (Bello Wang)

 

AGOA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
AGOA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.