ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
AGOA

Dokar tabbatar da karuwar tattalin arziki da damar raya nahiyar Afirka (AGOA) muhimmiyar doka ce ta kasar Amurka, a fannin samar da gatancin ciniki ga kasashen Afirka. Kana an dade ana kallonta a matsayin tushen huldar Afirka da Amurka ta fuskar tattalin arziki. Amma a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata, wa’adin dokar ya cika, ko da yake dimbin kasashen dake nahiyar Afirka sun yi ta kira da a tsawaita wa’adin dokar. Wannan batu ya nuna ra’ayin kasar Amurka dangane da kasashen Afirka, wato ko-in-kula.

 

A shekarar 2000, gwamnatin Bill Clinton ta sa aka zartas da dokar AGOA da zummar zurfafa alakar ciniki tsakanin kasar Amurka da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara. Wannan doka ta shafi kasashe 32, inda aka ba su damar fitar da nau’ikan kayayyaki fiye da dubu daya zuwa kasar Amurka. Sa’an nan a shekarar 2023, wato shekara ta karshe da ake iya samun alkaluma masu nasaba da dokar, kasashen Afirka sun fitar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 9.7 zuwa kasar Amurka, bisa sharadin gatanci da aka tanada cikin dokar AGOA.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulkin kasar Amurka a farkon bana, yanayi ya sauya: An fara karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin kasashen Afirka da ake shigar da su kasar Amurka, da rufe hukumar samar da agaji a duniya ta kasar Amurka ta USAID, gami da barin wa’adin dokar AGOA ta cika ba tare da tsawaita shi ba a wannan karo. A hannu daya, kasar Amurka ta janye gatanci da tallafin da ta ba kasashen Afirka a baya, kana a dayan hannun, tana neman samun karin kudi daga wajensu, hakan ya kara raunana ayyukan masana’antun Afirka wanda ko da ma ba su da karfi. Bisa gargadin da hukumar kula da ciniki da ci gaban tattalin arziki ta Majalisar Dinkin Duniya (UNCTAD) ta gabatar a kwanan baya, rashin aikin dokar AGOA zai haddasa raguwar kayayyakin da ake fitar da su daga kasashen Afirka zuwa kasar Amurka sosai, musamman ma a kasashen Kenya, da Tanzania, da Madagascar, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

 

Yanzu haka, wasu shugabannin kasashen Afirka na kokarin lallashin masu fada-a-ji na kasar Amurka don su taimaka wajen tabbatar da tsawaitar wa’adin dokar AGOA. Kana wani jami’in fadar White House ta kasar Amurka shi ma ya ce akwai yiwuwar kara wa’adin da shekara daya. Sai dai karin harajin fito da kasar Amurka ta saka ma kayayyakin dimbin kasashen dake nahiyar Afirka ya riga ya kawar da ma’anar gatancin da dokar AGOA ta kunsa. Ban da haka ana shakku kan ko gwamnatin Trump na da sahihanci wajen tsawaita wa’adin dokar AGOA. A cewar Farhana Paruk, masaniyar ilimin al’amuran kasa da kasa ta kasar Afirka ta Kudu, gwamnatin Trump ka iya amfani da batun wajen matsawa kasashen Afirka lamba, don neman biyan bukatarta ta fuskar harkokin siyasa.

 

A zahiri, ra’ayin gwamnatin kasar Amurka na yanzu dangane da kasashen Afirka, ya kara zama na ko-in-kula, idan an kwatanta shi da na gwamnatin kasar na lokacin baya. Dalilin da ya sa ake samun wannan sauyi, shi ne raguwar karfin kasar Amurka, da tasirinta a duniya. A baya, kasar dake da imani kan makomarta ta iya samar da moriya ga sauran kasashe, don musayar goyon bayansu. Amma a zamanin yanzu, kasar Amurka tana kallon sauran kasashe a matsayin “masu samar mata da jini”, inda take lura da moriya ta gajeren lokaci kawai, maimakon adalci da abokantaka. (Bello Wang)

 

AGOA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
AGOA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.