ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
AGOA

Dokar tabbatar da karuwar tattalin arziki da damar raya nahiyar Afirka (AGOA) muhimmiyar doka ce ta kasar Amurka, a fannin samar da gatancin ciniki ga kasashen Afirka. Kana an dade ana kallonta a matsayin tushen huldar Afirka da Amurka ta fuskar tattalin arziki. Amma a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata, wa’adin dokar ya cika, ko da yake dimbin kasashen dake nahiyar Afirka sun yi ta kira da a tsawaita wa’adin dokar. Wannan batu ya nuna ra’ayin kasar Amurka dangane da kasashen Afirka, wato ko-in-kula.

 

A shekarar 2000, gwamnatin Bill Clinton ta sa aka zartas da dokar AGOA da zummar zurfafa alakar ciniki tsakanin kasar Amurka da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara. Wannan doka ta shafi kasashe 32, inda aka ba su damar fitar da nau’ikan kayayyaki fiye da dubu daya zuwa kasar Amurka. Sa’an nan a shekarar 2023, wato shekara ta karshe da ake iya samun alkaluma masu nasaba da dokar, kasashen Afirka sun fitar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 9.7 zuwa kasar Amurka, bisa sharadin gatanci da aka tanada cikin dokar AGOA.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulkin kasar Amurka a farkon bana, yanayi ya sauya: An fara karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin kasashen Afirka da ake shigar da su kasar Amurka, da rufe hukumar samar da agaji a duniya ta kasar Amurka ta USAID, gami da barin wa’adin dokar AGOA ta cika ba tare da tsawaita shi ba a wannan karo. A hannu daya, kasar Amurka ta janye gatanci da tallafin da ta ba kasashen Afirka a baya, kana a dayan hannun, tana neman samun karin kudi daga wajensu, hakan ya kara raunana ayyukan masana’antun Afirka wanda ko da ma ba su da karfi. Bisa gargadin da hukumar kula da ciniki da ci gaban tattalin arziki ta Majalisar Dinkin Duniya (UNCTAD) ta gabatar a kwanan baya, rashin aikin dokar AGOA zai haddasa raguwar kayayyakin da ake fitar da su daga kasashen Afirka zuwa kasar Amurka sosai, musamman ma a kasashen Kenya, da Tanzania, da Madagascar, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

 

Yanzu haka, wasu shugabannin kasashen Afirka na kokarin lallashin masu fada-a-ji na kasar Amurka don su taimaka wajen tabbatar da tsawaitar wa’adin dokar AGOA. Kana wani jami’in fadar White House ta kasar Amurka shi ma ya ce akwai yiwuwar kara wa’adin da shekara daya. Sai dai karin harajin fito da kasar Amurka ta saka ma kayayyakin dimbin kasashen dake nahiyar Afirka ya riga ya kawar da ma’anar gatancin da dokar AGOA ta kunsa. Ban da haka ana shakku kan ko gwamnatin Trump na da sahihanci wajen tsawaita wa’adin dokar AGOA. A cewar Farhana Paruk, masaniyar ilimin al’amuran kasa da kasa ta kasar Afirka ta Kudu, gwamnatin Trump ka iya amfani da batun wajen matsawa kasashen Afirka lamba, don neman biyan bukatarta ta fuskar harkokin siyasa.

 

A zahiri, ra’ayin gwamnatin kasar Amurka na yanzu dangane da kasashen Afirka, ya kara zama na ko-in-kula, idan an kwatanta shi da na gwamnatin kasar na lokacin baya. Dalilin da ya sa ake samun wannan sauyi, shi ne raguwar karfin kasar Amurka, da tasirinta a duniya. A baya, kasar dake da imani kan makomarta ta iya samar da moriya ga sauran kasashe, don musayar goyon bayansu. Amma a zamanin yanzu, kasar Amurka tana kallon sauran kasashe a matsayin “masu samar mata da jini”, inda take lura da moriya ta gajeren lokaci kawai, maimakon adalci da abokantaka. (Bello Wang)

 

AGOA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
AGOA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.