• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar: NIS Ta Dage Takunkumin Shige Da Fice

ACG Sunday James Ya Garzaya Yankin Yobe Da Borno Don Tabbatarwa

by yahuzajere
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar: NIS Ta Dage Takunkumin Shige Da Fice
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon umarnin da Gwamnatin Tarayya ta bayar na sake buɗe iyakokin Nijeriya da Nijar, Shugabar Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa,  CGI Kemi Nanna Nandap ta Umarci dukkan kwanturololin jihohi da na kula da iyakoki da ke gefen iyakokin Nijeriya da Nijar su tabbatar da aiwatarwa.

Shugabar hukumar ta umarci kwanturololin su ɗage takunkumin shige da ficen mutane da kayayyaki a iyakokin.

Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma cewa a shirye take wajen kula da shige da fice a kan iyakokin Ƙasa bisa ƙa’ida tare da kiyaye mutunci da tsaron iyakokin Nijeriya.

Babban Shugaban Shiyya ta Uku (Zone C), da ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato, Mataimakin Kwanturola Janar (ACG) James Sunday, ya kai ziyarar aiki a jihohin Borno da Yobe da ke Arewa maso Gabas domin lura da yadda ake bude iyakar.

nijar

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

CGI Kemi Nanna Nandap

A cewar ACG Sunday James, ya garzaya sansanonin gudanar da ayyukan hukumar domin ganin an dauki matakin da ya dace na tabbatar da bude iyakokin ga jama’a ba kuma tare da kawo matsala ga tsaron kasa ba.

A cewar ACG Sunday James, “An sanar da Kwanturola na Yobe da Borno kan wannan umarni, na zo nan a matsayina na shugaban shiyyarsu domin tabbatar da cikakkiyar aiwatar da umarni, tare da tabbatar wa jama’a jajircewarmu wajen tabbatar da tsaron kasa ta hanyar shige da ficen iyakoki a kan ka’ida domin kiyaye mutunci da tsaron ‘Yan Nijeriya.

nijar
Tawagar ACG Sunday James tare da Gwamna Buni da manyan jami’an Gwamnatin Yobe

 

A ranar Laraba ne gwamnatin tarayyar Nijeriya ta umurci hukumomin tsaron kan iyakokin da abin ya shafa da su bude kan iyakar Nijeriya da Nijar a wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Ajuri Ngelale ya Sanya wa hannu.

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin Nijeriya ta kasa da ta sama da jamhuriyar Nijar tare da dage wasu takunkumin da aka kakabawa kasar nan take.

A cewar sanarwar ta Ajuri Ngelale, umarnin ya yi daidai da shawarar da Kungiyar ECOWAS ta yanke a babban taronta na musamman da ta yi a ranar 24 ga watan Fabrairun 2024 a Abuja.

nijar

Shugabannin ECOWAS sun amince da dage takunkumin karya tattalin arziki da suka kakaba wa Jamhuriyar Nijar, Mali, Burkina Faso, da Guinea.

Daga cikin takunkuman da aka kakaba wa Jamhuriyar Nijar da shugaban kasa ya ba da umarnin dagewa nan take, akwai:

(1) Rufe iyakokin kasa da ta sama tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, da kuma hana zirga-zirgar jiragen sama a yankunan kasashen ECOWAS daga Nijar zuwa cikinsu ko daga cikinsu zuwa can.

(2) Dakatar da duk wasu hada-hadar kasuwanci da hada-hadar kudi tsakanin Nijeriya da Nijar, da kuma dakatar da duk wasu ayyuka na musamman kamar samar da wuta lantarki ga Jamhuriyar Nijar.

nijar

(3) Rufe kadarorin Jamhuriyar Nijar a Babban Bankin ECOWAS da kadarorin kasar na kamfanonin gwamnati, da ma’aikatu a bankunan kasuwanci.

(4) Dakatar da bai wa Nijar duk wani tallafi na kudi da mu’amala da duk hukumomin kudi, musamman.

(5) Hana tafiye-tafiye ga jami’an gwamnati da iyalansu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASIyakokin KasaNijarNijeriyaTakunkumi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Gwamna Dauda Ya Biya Ma’aikatan Zamfara Kuɗin Hutu Don Kyautata Walwalarsu

Next Post

Mai Sana’ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

4 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

23 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
Mai Sana’ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

Mai Sana'ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

LABARAI MASU NASABA

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.