ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar: NIS Ta Dage Takunkumin Shige Da Fice

ACG Sunday James Ya Garzaya Yankin Yobe Da Borno Don Tabbatarwa

by yahuzajere
2 years ago
nijar

Sakamakon umarnin da Gwamnatin Tarayya ta bayar na sake buɗe iyakokin Nijeriya da Nijar, Shugabar Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa,  CGI Kemi Nanna Nandap ta Umarci dukkan kwanturololin jihohi da na kula da iyakoki da ke gefen iyakokin Nijeriya da Nijar su tabbatar da aiwatarwa.

Shugabar hukumar ta umarci kwanturololin su ɗage takunkumin shige da ficen mutane da kayayyaki a iyakokin.

Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma cewa a shirye take wajen kula da shige da fice a kan iyakokin Ƙasa bisa ƙa’ida tare da kiyaye mutunci da tsaron iyakokin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Babban Shugaban Shiyya ta Uku (Zone C), da ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato, Mataimakin Kwanturola Janar (ACG) James Sunday, ya kai ziyarar aiki a jihohin Borno da Yobe da ke Arewa maso Gabas domin lura da yadda ake bude iyakar.

nijar

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

CGI Kemi Nanna Nandap

A cewar ACG Sunday James, ya garzaya sansanonin gudanar da ayyukan hukumar domin ganin an dauki matakin da ya dace na tabbatar da bude iyakokin ga jama’a ba kuma tare da kawo matsala ga tsaron kasa ba.

A cewar ACG Sunday James, “An sanar da Kwanturola na Yobe da Borno kan wannan umarni, na zo nan a matsayina na shugaban shiyyarsu domin tabbatar da cikakkiyar aiwatar da umarni, tare da tabbatar wa jama’a jajircewarmu wajen tabbatar da tsaron kasa ta hanyar shige da ficen iyakoki a kan ka’ida domin kiyaye mutunci da tsaron ‘Yan Nijeriya.

nijar
Tawagar ACG Sunday James tare da Gwamna Buni da manyan jami’an Gwamnatin Yobe

 

A ranar Laraba ne gwamnatin tarayyar Nijeriya ta umurci hukumomin tsaron kan iyakokin da abin ya shafa da su bude kan iyakar Nijeriya da Nijar a wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Ajuri Ngelale ya Sanya wa hannu.

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin Nijeriya ta kasa da ta sama da jamhuriyar Nijar tare da dage wasu takunkumin da aka kakabawa kasar nan take.

A cewar sanarwar ta Ajuri Ngelale, umarnin ya yi daidai da shawarar da Kungiyar ECOWAS ta yanke a babban taronta na musamman da ta yi a ranar 24 ga watan Fabrairun 2024 a Abuja.

nijar

Shugabannin ECOWAS sun amince da dage takunkumin karya tattalin arziki da suka kakaba wa Jamhuriyar Nijar, Mali, Burkina Faso, da Guinea.

Daga cikin takunkuman da aka kakaba wa Jamhuriyar Nijar da shugaban kasa ya ba da umarnin dagewa nan take, akwai:

(1) Rufe iyakokin kasa da ta sama tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, da kuma hana zirga-zirgar jiragen sama a yankunan kasashen ECOWAS daga Nijar zuwa cikinsu ko daga cikinsu zuwa can.

(2) Dakatar da duk wasu hada-hadar kasuwanci da hada-hadar kudi tsakanin Nijeriya da Nijar, da kuma dakatar da duk wasu ayyuka na musamman kamar samar da wuta lantarki ga Jamhuriyar Nijar.

nijar

(3) Rufe kadarorin Jamhuriyar Nijar a Babban Bankin ECOWAS da kadarorin kasar na kamfanonin gwamnati, da ma’aikatu a bankunan kasuwanci.

(4) Dakatar da bai wa Nijar duk wani tallafi na kudi da mu’amala da duk hukumomin kudi, musamman.

(5) Hana tafiye-tafiye ga jami’an gwamnati da iyalansu.

 

nijar
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Mai Sana’ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

Mai Sana'ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.