• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Lantarki

LABARAI MASU NASABA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

‘Yan Nijeriya sun fara azumin wata Ramadana a bana cikin matsanancin rashin wutar lantarki a daidai lokacin da ake fuskantar matukar zafi a kasar.

Da ma dai kasar ta dade tana fama da matsalar wadatacciyar wutar lantarki, sai dai bayanan sun nuna cewa a wannan lokaci rashin wutar lantarkin ya yi matukar karuwa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

A wannan karon dai, gwamnatin Nijeriya ta dora alhakkin karancin wutar lantarkin kan rashin isasshiyar iskar gas. Abin da ya sa ko a watan jiya ma’aikatar wutar lantarkin tare da hadin gwiwar ma’aikatar albarkatun man fetur na kasar nan suka kafa wani kwamiti domin ya lalubo hanyar magance karancin gas da kamfanonin samar da wutar lantarki ke fama da shi.

Sannan a daya bangaren kuma, akwai matsalar lalata manyan turakun wutar lantarki wanda ake zargin wasu bata-gari suna yi. Na baya-bayan nan shi ne na lalacewar babban layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Katampe kamar yadda babbar jami’ar hulda da jama’a ta kamfanin rarraba wutar lantarki (TCN), Ndidi Mbah ta bayyana.

Misis Mbah ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya cewa, wannan ne karon na biyar da ake samun irin wannan matsalar ta katsewar babban layin wutar lantarki tsakanin watan Fabrairu zuwa Maris.

Sai dai shugaban kamfanin SkyMark Energy and Power Ltd, Muhammad Sale Hassan, sannan ya kasance mai sharhi kan harkokin makamashi yana ganin cewa wannan laifin na kamfanoni masu zaman kansu ne (Discos), wadanda suke rarraba wutar lantarki.

Ya ce kamfanonin ba su da kwarewa da isasshen karfin jari da za su iya ci gaba da gudanar da aikin rarraba wutar lantarki. Sai dai kamfanonin sun sha musanta irin wadannan zargi da ake musu.

Mai sharhin ya ce suna samun matsala ne a bargaren rarraba wutar lantarki, amma ba a bangaren samar da ita ba.

Ko a makon jiya ma, ministan wutar lantarki na Nijeriya, Bayo Adelabu ya yi barazanar kwace lasisin kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasar nan, saboda yawan dauke-dauken wutan da ake yi. Yana mai cewa ba za a lamunci yanayin da suke saka mutane na karancin wutar lantarki ba a fadin kasar nan.

Sai dai masana na ganin cewa dole ne gwamnatin Nijeriya ta shafa wa fuskarta toka idan tana so ta kawo karshen matsalar wutar lantarki, domin kuwa da wahala muradinta na samar da ci gaba a kasar ya cika muddin ba a samar da isasshen hasken wutar lantarki ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole
Labarai

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Next Post
Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al'ummar Nafada A Jihar Gombe

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.