• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Dalibai biyu na Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a lokacin da suke ƙoƙarin karbar kayan abinci da gwamnatin Jihar ta ba su a matsayin tallafi don rage radadin tsadar rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki a Nijeriya.

Daliban da ba a bayyana sunayensu ba, sun rasu a safiyar yau Juma’a yayin karbar kayan abincin tallafin.

  • An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa
  • Rundunar ‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Kama Kungiyar Da Ta Sace Kananan Yara 45 

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa daliban da abin ya shafa mata ne, ko da yake majiyar ta ce wasu da dama sun samu raunuka daban-daban a yayin da abun ya faru a wurin taron rabon kayan abincin.

Shugaban kungiyar daliban jihar Nasarawa, Yunusa Yusuf Baduku, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa domin kula da lafiyarsu.

Sai dai Baduku bai iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba nan take.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

“Hakika abin da ya faru da safiyar yau a Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, lamarin abun tausayi ne.

“Bayan shirin da muka yi na rabon kayan abinci ga daliban da za a yi a Jami’ar, kwatsam sai ga su (daliban) sun isa wurin da yawansu, suka kuma yi nasara kan jami’an tsaro da ke wurin.

“Sun kutsa kai cikin wurin da ake rabon, abin bakin ciki shi ne yawancin dalibanmu mata sun samu raunuka da dama, yayin da wasu kuma suka shanye saboda yawan jama’a da ke wurin rabo kayan tallafin.

“A yanzu haka ina cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke garin Keffi, inda muka kawo wasu dalibanmu domin ba su kulawar gaggawa, bazan iya tabbatar da alkaluman wadanda suka jikkata ba a halin yanzu, saboda wasunsu suna asibitin makarantar yayin da wasu kuma suna asibitin makarantar, wasu suna nan a FMC, Keffi suna karbar magani,” a acewarsa.

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Abdullahi Sule ya kara raba kayan tallafi ga daliban manyan makarantun jihar.

Gwamnatin jihar ta fara rabon shinkafa mai nauyin kilogiram 7:5 ga dalibai da ke Lafia babban birnin jihar a ranar Talata.

An rawaito cewa, an kuma ba kowane dalibi kudi naira 5,000 wanda ya kai naira miliyan 35 tare da kayan abinci.

Daliban da suka amfana da rabon sun fito ne daga Jami’ar Tarayya ta Lafia, Isa Mustapha Agwai Polytechnic Lafia, Kwalejin Aikin Gona Kimiyya da Fasaha ta Lafiya da kuma Makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Lafia.

Gwamna Sule ya yi alkawarin za a mika irin wannan tallafin ga wasu cibiyoyin da ke wajen babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'ar Jihar NasarawaMutuNasarawaRasu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bodejo A Gaban Kotu Kan Zargin Ta’addanci

Next Post

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Related

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Manyan Labarai

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

8 hours ago
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Manyan Labarai

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

9 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

21 hours ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

1 day ago
Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku
Manyan Labarai

Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

1 day ago
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

1 day ago
Next Post
Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa - Ngelzarma

LABARAI MASU NASABA

Tawagar FCT Na Ci Gaba da Lashe Lambobin Yabo a Gasar Wasanni Ta Ƙasa 

Tawagar FCT Na Ci Gaba da Lashe Lambobin Yabo a Gasar Wasanni Ta Ƙasa 

May 23, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

May 23, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Amince Da Lasisin Aikin Hakar Mai A Arewa

May 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu

Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu

May 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Zai Bibiyi Kwazon Ministocinsa A Ranar 29 Ga Watan Mayu

May 23, 2025
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

May 23, 2025
Gwamnan Kano Ya Ceto Dalibai 84 Da Ganduje Yaki Biya Wa Kudin Makaranta A Cyprus

Gwamnan Kano Ya Ceto Dalibai 84 Da Ganduje Yaki Biya Wa Kudin Makaranta A Cyprus

May 23, 2025
Nijeriya Ba Za Ta Taba Maimaita Yakin Basasa Na Shekarar 1967 —el-Rufai

El-Rufai Ya Zargi Bangaren Shari’a Da Cin Hanci Da Rashawa

May 23, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

May 23, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.