• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Dalibai biyu na Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a lokacin da suke ƙoƙarin karbar kayan abinci da gwamnatin Jihar ta ba su a matsayin tallafi don rage radadin tsadar rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki a Nijeriya.

Daliban da ba a bayyana sunayensu ba, sun rasu a safiyar yau Juma’a yayin karbar kayan abincin tallafin.

  • An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa
  • Rundunar ‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Kama Kungiyar Da Ta Sace Kananan Yara 45 

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa daliban da abin ya shafa mata ne, ko da yake majiyar ta ce wasu da dama sun samu raunuka daban-daban a yayin da abun ya faru a wurin taron rabon kayan abincin.

Shugaban kungiyar daliban jihar Nasarawa, Yunusa Yusuf Baduku, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa domin kula da lafiyarsu.

Sai dai Baduku bai iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba nan take.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

“Hakika abin da ya faru da safiyar yau a Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, lamarin abun tausayi ne.

“Bayan shirin da muka yi na rabon kayan abinci ga daliban da za a yi a Jami’ar, kwatsam sai ga su (daliban) sun isa wurin da yawansu, suka kuma yi nasara kan jami’an tsaro da ke wurin.

“Sun kutsa kai cikin wurin da ake rabon, abin bakin ciki shi ne yawancin dalibanmu mata sun samu raunuka da dama, yayin da wasu kuma suka shanye saboda yawan jama’a da ke wurin rabo kayan tallafin.

“A yanzu haka ina cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke garin Keffi, inda muka kawo wasu dalibanmu domin ba su kulawar gaggawa, bazan iya tabbatar da alkaluman wadanda suka jikkata ba a halin yanzu, saboda wasunsu suna asibitin makarantar yayin da wasu kuma suna asibitin makarantar, wasu suna nan a FMC, Keffi suna karbar magani,” a acewarsa.

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Abdullahi Sule ya kara raba kayan tallafi ga daliban manyan makarantun jihar.

Gwamnatin jihar ta fara rabon shinkafa mai nauyin kilogiram 7:5 ga dalibai da ke Lafia babban birnin jihar a ranar Talata.

An rawaito cewa, an kuma ba kowane dalibi kudi naira 5,000 wanda ya kai naira miliyan 35 tare da kayan abinci.

Daliban da suka amfana da rabon sun fito ne daga Jami’ar Tarayya ta Lafia, Isa Mustapha Agwai Polytechnic Lafia, Kwalejin Aikin Gona Kimiyya da Fasaha ta Lafiya da kuma Makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Lafia.

Gwamna Sule ya yi alkawarin za a mika irin wannan tallafin ga wasu cibiyoyin da ke wajen babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'ar Jihar NasarawaMutuNasarawaRasu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bodejo A Gaban Kotu Kan Zargin Ta’addanci

Next Post

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Related

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

10 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

12 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

16 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

17 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

22 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 day ago
Next Post
Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa - Ngelzarma

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.