ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

by Muhammad
2 years ago
Nasarawa

Wasu Dalibai biyu na Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a lokacin da suke ƙoƙarin karbar kayan abinci da gwamnatin Jihar ta ba su a matsayin tallafi don rage radadin tsadar rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki a Nijeriya.

Daliban da ba a bayyana sunayensu ba, sun rasu a safiyar yau Juma’a yayin karbar kayan abincin tallafin.

  • An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa
  • Rundunar ‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Kama Kungiyar Da Ta Sace Kananan Yara 45 

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa daliban da abin ya shafa mata ne, ko da yake majiyar ta ce wasu da dama sun samu raunuka daban-daban a yayin da abun ya faru a wurin taron rabon kayan abincin.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar daliban jihar Nasarawa, Yunusa Yusuf Baduku, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa domin kula da lafiyarsu.

Sai dai Baduku bai iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba nan take.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Hakika abin da ya faru da safiyar yau a Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, lamarin abun tausayi ne.

“Bayan shirin da muka yi na rabon kayan abinci ga daliban da za a yi a Jami’ar, kwatsam sai ga su (daliban) sun isa wurin da yawansu, suka kuma yi nasara kan jami’an tsaro da ke wurin.

“Sun kutsa kai cikin wurin da ake rabon, abin bakin ciki shi ne yawancin dalibanmu mata sun samu raunuka da dama, yayin da wasu kuma suka shanye saboda yawan jama’a da ke wurin rabo kayan tallafin.

“A yanzu haka ina cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke garin Keffi, inda muka kawo wasu dalibanmu domin ba su kulawar gaggawa, bazan iya tabbatar da alkaluman wadanda suka jikkata ba a halin yanzu, saboda wasunsu suna asibitin makarantar yayin da wasu kuma suna asibitin makarantar, wasu suna nan a FMC, Keffi suna karbar magani,” a acewarsa.

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Abdullahi Sule ya kara raba kayan tallafi ga daliban manyan makarantun jihar.

Gwamnatin jihar ta fara rabon shinkafa mai nauyin kilogiram 7:5 ga dalibai da ke Lafia babban birnin jihar a ranar Talata.

An rawaito cewa, an kuma ba kowane dalibi kudi naira 5,000 wanda ya kai naira miliyan 35 tare da kayan abinci.

Daliban da suka amfana da rabon sun fito ne daga Jami’ar Tarayya ta Lafia, Isa Mustapha Agwai Polytechnic Lafia, Kwalejin Aikin Gona Kimiyya da Fasaha ta Lafiya da kuma Makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Lafia.

Gwamna Sule ya yi alkawarin za a mika irin wannan tallafin ga wasu cibiyoyin da ke wajen babban birnin jihar.

Nasarawa
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa - Ngelzarma

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.