• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kaddamar da shirin rabon kayan abinci na watan Ramadan, domin a rage radadin wahalhalu ga al’ummar jihar.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabinsa na kaddamar da rabon abincin don ci gaban manufofin jin-kai na gwamnatinsa.

  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa
  • ÆŠaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun KarÉ“ar Abincin Tallafi

A yayin da yake bayyanawa taron jama’ar cewa” gwamntinsa ta yi hakan ne daga jama’a don taimaka wa mabukata da kuma bayar da agaji ga wadanda matsalolin zamantakewa da tattalin arziki ya shafa.

“Hanya ce ta nuna hadin kai da goyon baya ga jama’a da kuma yadda za su iya samun albarkatu don ci gaban rayuwarsu.

“Wannan alama ce ta al’umma da kuma zama majibincin É—an uwan juna.”

Labarai Masu Nasaba

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

A cewar gwamnan, rabon hatsin shi ma wani mataki ne na wucin gadi na samar da tallafi ga al’ummar jihar baki daya.

Ya kuma umarci duk wadanda aka damka wa hatsin da su tabbatar an bai wa daukacin al’ummar jihar kasonsu.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Jihar Kebbi ita ce gwamnatin al’umma, don haka ya kamata a raba kayan abinci ba tare da nuna bambancin addini ko kabilancin ba.

“Siyasa ta kare, an gama zabe, abin da ya rage shi ne shugabanci na gari, bai kamata a bar kowa ba, babu bambancin jam’iyya.

Ya kuma gargadi kwamitocin rabon kayayyaki a dukkan matakai kan duk wani nau’i na mataki kar a siyar da su, ko kuma karkatar da hatsin da aka yi tanadi don mutanen jihar.

Ya kuma yi gargadin cewa duk wani jami’in gwamnati da aka samu yana karkatar da hatsi za a hukunta shi, wanda zai kai ga tsige shi daga mukaminsa, ya kuma umarci shugabannin hukumomin tsaro da su tabbatar da bin ka’ida gaba daya ko kuma a kama duk wanda aka samu da laifi a hukunta shi.

Tun da farko kwamishinan noma, Alhaji Shehu Mu’azu ya yaba wa gwamnan bisa amincewa da sayan buhunan iri-iri domin jin dadin jama’arsa.

Ya kuma yaba da kyawawan halayen Gwamna Nasir Idris zuwa ga jama’ar jih6ar Kebbi kan wannan tsari da ya kaddamar na rabon abinci a duk fadin jihar.

Mu’azu ya sanar wa mahalarta taron cewa abin da aka kaddamar don rabawa kashi ashirin ne na hatsin da gwamnati ta saya yayin da za a yi rabon sauran a ma’auni daga baya a matakai.

Ya ce tuni aka aike da hatsin da ke tara a dukkanin kananan hukumomin 21 zuwa hedikwatar kananan hukumomin don raba wa ga al’ummar yankunan.

Daga karshe Kwamishinan ya bayyana irin kayan abincin da gwamnatin jihar ta sayo don rabawa ga watan azumin Ramadana sun hada da Gero, dawa da kuma shinkafa da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna NasirKebbirabon kayan abinciRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Next Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

59 minutes ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

2 hours ago
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
Labarai

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

6 hours ago
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
Labarai

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

9 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

10 hours ago
Next Post
sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa WaÉ—anda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa WaÉ—anda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.