• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane kalilan ne suka san shi a shekarar da ta wuce, amma yanzu ya shirya zama shugaban kasa.

Tashen ban al’ajabi na Bassirou Diomaye Faye, wani lokaci ne mai cike da hawa da gangara a tarihin siyasar Senegal, da kuma ya zo da mamaki ga mutane da dama.

  • Idan Aka Fatattaki ‘Yan Ta’adda Daga Zamfara Duk Arewa Za Mu Samu Sauki – Gwamna Dauda
  • Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Watannin da ya shafe tsare a gidan yari tare da babban abokin siyasarsa kuma uban-gidansa Ousmane Sonko sun zo karshe a yayin da ya rage mako daya a yi zaben shugaban kasar.

A yanzu Mai gaskiya, kamar yadda ake yi masa lakabi, zai iya fara aiki kan manyan sauye-sauyen da ya yi alkawarin kawowa a lokacin yakin neman zabe.

“Mai tabbatar da bin tsari” da “kas-kas da kai” su ne kalmomin da aka fi amfani da su wajen bayyana jami’in karbar harajin, wanda ke bikin cikarsa shekara 44 da haihuwa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Mallam Faye cikin murna ya kan tuna rayuwar kuruciyarsa ta kauye a Ndiaganiao, inda ya ce ya kan kai ziyara a duk ranar Lahadi don yin aiki a gona.

Kaunarsa da darajar da yake bai wa rayuwar mutanen karkara sun dace da zuzzurfan rashin amincewarsa da manyan kasa a Senegal da kuma tsarin siyasar da aka saba da ita.

“Bai taba rike mukamin minista ba, kuma shi ba gogaggen jami’in gwamnati ba ne don haka masu suka suke tuhumar rashin gogewarsa,” kamar yadda mai sharhi Alioune Tine ya faka wa BBC.

“Sai dai, fahimtar Faye, jami’an da suka tafiyar da harkokin mulkin kasar tun daga 1960 sun tafka manya-manyan kura-kurai.”
Yaki da fatara da rashin adalci da kuma cin hanci na cikin manyan manufofin Mallam Faye. Da yake aiki a Baitulmali, shi da Ousmane Sonko sun kafa wata kungiyar ko-ta-kwana don tunkarar masu cin hanci da rashawa.

Yarjeniyoyin hakar iskar gas da man fetur da kuma na tsaro jazaman ne sai an sake cimma matsaya a kan su don su biya muradan al’ummar Senegal, in ji Mallam Faye.

Yana kokarin kawo wani zamani na “gwamnati mai cikakken iko da “birkita al’amura” sabanin yadda aka saba yi a baya, kamar yadda ya faka wa masu zabe, da kuma mu-samman hakikanin alakarsu da Faransa.

Zababben shugaban kasar na Senegal ya ce zai yi watsi da kudin saifa na Faransa da ake yawan sukar lamiri, wadda ake kwatanta darajarta da yuro sannan take samun goyon bayan Faransa, tsohuwar uwargijiyar mulkin mallakar Senegal.

Mallam Faye dai yana son maye gurbin saifa da wani sabon kudin Senegal ko na yankin Afirka ta Yamma, ko da yake hakan ba abu ne mai sauki ba.

“Zai ci karo da kalubalen hakikanin al’amura kamar na kasafin kudin a farkon farawa… Sai dai na lura shi mutum ne mai kumbin buri,” tsohuwar Firaminista Aminata Toure wadda ta yi aiki a karkashin shugaba mai barin gado Macky Sall ta bayyana wa BBC.

Karfafa ‘yancin cin gashin kai ga bangaren shari’a da samar da ayyuka ga dumbin mata-san Senegal su ma suna cikin manyan manufofin Mallam Faye – dukkansu biyun dai “ba su samu wata kyakkyawar kulawa ba daga Shugaba Sall, alhakin hakan kuma sai da ya kama shi”, Aminata Toure ta kara da cewa.

Ba ita ce kadai babbar ‘yar siyasa da ta mara baya ga matashin kan shekara 44 ba – tsohon shugaban kasar Abdoulaye Wade shi ma ya yi hakan kwana biyu kacal kafin zaben ranar Lahadi.

Wani gagarumin sauyin rayuwa ne ga Mallam Faye bayan ya shafe wata 11 da ya wuce tsare a gidan yari bisa tuhume-tuhumen bore da kuma shekaru da dama kafin nan a karkashin siyasar abokiyar tafiyarsa.
‘Bassirou da ni abu daya ne’.

A cikin watan Fabrairu ne aka sanar da Bassirou Diomaye Faye a matsayin abin da aka kira kan takarar “idan hagu ta kiya, a koma dama”, don maye gurbin jagoran ‘yan adawa mai kwarjini da kwakwazo, Osumane Sonko. “Zan iya cewa ya fi ni kokarin kamanta gaskiya,” Sonko ya ce cikin alfahari.

Su biyun ne suka kafa rusasshiyar jam’iyyar Pastef, su biyun kuma sun kasance jami’an karbar haraji, kuma dukkansu sun samu kansu a gidan kurkuku bara a kan tuhume-tuhumen da suka ce suna da alaka da siyasa.
A karshe dai an samu Ousmane Sonko da aikata laifuka guda biyu, abin da ke nufin hana masa damar tsayawa takara a zabe, don haka sai Mallam Faye ya shige gaba.
“Ni da Bassirou duk daya ne,” Mallam Sonko ya fada wa taron magoya baya cikin ‘yan kwanakin nan. “Manyan aminan juna ne,” in ji Moustapha Sarre wani takwaransu a jam’iyyar Pastef ya bayyana.

Hakan ta sanya ana sukar lamirin cewa Mallam Faye kawai zai kasance ne “shugaban kasa ne na je-ka-na-yi-ka”.

Ba lallai hakan ta kasance ba, a cewar mai sharhi Mista Tine. Sai dai dangantakar mu-tanen biyu za ta iya kawo wani sabon salon shugabanci a Senegal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

Next Post

A Kawo Dauki Don Magance Tsadar Kudin Zuwa Aikin Hajjin Bana

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

10 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

11 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
Bassirou Diomaye Faye
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

16 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

17 hours ago
Next Post
hajjin 2024

A Kawo Dauki Don Magance Tsadar Kudin Zuwa Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.