ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Aka Fatattaki ‘Yan Ta’adda Daga Zamfara Duk Arewa Za Mu Samu Sauki – Gwamna Dauda

by Bello Hamza
2 years ago
Maulidi

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya koka ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a kan karuwar harkokin ta’addanci a Jihar Zamfara, yana mai cewa, in har aka samu nasarar fattakar ‘yan ta’adda a Jihar Zamfara tamkar an kore su ne daga yankin arewa gaba daya.

Gwamnan ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da manema labarai a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Talata. Ya kuma kara da cewa, barin ‘yan ta’adda na cin karensu babu babbaka a yankin Zamfara yankin arewa gaba daya zai ci gaba da kasancewa a cikin hadari.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Da Takwaransa Na Kasar Kazakhstan Sun Mika Sakwannin Murnar Kaddamar Da “Shekarar Yawon Bude Ido Ta Kazakhstan” A Sin
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Gana Da Ministan Ruwa Domin Kammala Ayyukan Ruwa A Zamfara

Daga na Gwamna Lawal ya kuma ce, “A yau a mastayina na Gwamnan Jihar Zamfara na zo fadar shugaban kasa (villa) inda na gana da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu domin na yi masa bayanin irin matsalolin da muke fuskanta na rashin tsaro a Jihar Zamfara, wanda kuma tattunawar tamu ta yi amfani kwarai da gaske, domin ya bani tabbacin cewa, da ikon Allah zai yi duk abin da zai yi ya taimaka mana a Jihar Zamfara don mu samu sauki. Saboda idan ka duba yanzu duk matsalolin tsaro da ake samu yanzu a kusa yankin arewa gaba daya abubuwa ne da suke tasowa daga Zamfara, saboda haka idan aka yi abin da ya kamata a yankin Zamfara kusan dukka yankin arewa za a samu sauki”
Ya kuma bayyana cewa. “Na ji dadin wannan tattauanwar na kuma yi farin ciki sosai. Haka kuma ya gamsu da dukkan bayanin da na yi masa a ka matsalolin da muke fuskanta a Zamfara na mastalar tsaro. Wasu matsalolin da na yi masa bayani a kai da can bai san dasu ba, amma yau ya san kusan komai da ke faruwa a wannan jihar ta mu”.

ADVERTISEMENT

Tun da ya dare karagar mulkin jihar ne, Gwamna Lawal yake fadi tashin ganin an samu zaman lafiya a jihar Zamfara. Cikin matakan da ya dauka akwai da kafa rundunar Askarawan Zamfara wanda aka shirya za su yi aiki kafada da kafada da jami’an tsaro don fatattakar ‘yan bindiga.

A kwanan nan ma ya ziyarci shugaban rundunar tsaro Janar CG Musa inda ya nemi a kara yawan sojojin da ke aiki a Zamfara don dakile ayyukan ‘yan ta’adda.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Zamfara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.