• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Da Joe Biden Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Da Joe Biden Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden a jiya Talata ta wayar tarho, bisa bukatar shugaba Biden. Shugabannin biyu sun yi tattaunawa mai zurfi da musayar ra’ayi kan dangantakar kasashensu da batutuwan da ke jan hankulansu.

Shugaba Xi ya bayyana cewa, ganawarsa da shugaba Biden a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, ya bude wata mahangar makomarsu. Ya ce cikin watannin da suka gabata, jami’an kasashen biyu sun aiwatar da matsayar da suka cimma sahihanci. Kuma dangantakar Sin da Amurka ta fara daidaituwa, sannan al’ummomin kasashen biyu da ma na kasa da kasa na maraba da hakan. Ya ce a daya bangaren, abubuwan dake yin mummunan tasiri kan dangantakarsu na karuwa, don haka akwai bukatar bangarorin biyu su mayar da hankali kan su.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Fadada Yankunan Tudu Na Teku Da Take Iko Da Su
  • Sin Ta Mai Da Martani Ga Yadda Amurka Ta Gyara Matakin Kayyade Fitar Da Kayayyakin Sassan Laturoni Zuwa Ketare

Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, batun Taiwan shi ne iyaka ta farko da bai kamata a tsallake ba a dangantakar kasashen biyu. Ya ce kasar Sin ba za ta nade hannu tana kallon ayyukan ‘yan aware masu neman ‘yancin yankin da tallafi da goyon bayan da ake ba su daga waje ba.

A nasa bangaren, shugaba Biden ya ce dangatakar Sin da Amurka ita ce mafi tasiri a duniya. Kuma ci gaban dangantakar da aka samu bayan ganawarsu ta San Francisco, ya nuna cewa bangarorin biyu za su iya inganta hadin gwiwarsu tare da hakuri da bambance-bambancen dake akwai tsakaninsu.

Joe Biden ya kuma nanata cewa, Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi ba ya nufin yi wa Sin taron dangi. Kazalika, Amurka ba ta goyon bayan ‘yancin yankin Taiwan, kuma ba ta neman tada rikici tsakaninta da Sin. Bugu da kari, ya ce Amurka tana goyon bayan manufar Sin daya tak a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya yi karin haske a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau, game da tattaunawa ta wayar tarho, tsakanin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, kan batutuwan sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, da yankin Hong Kong, da jihar Xinjiang, da ta Xizang da sauransu.

Game da batun sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, Wang Wenbin ya bayyana cewa, a yayin tattaunawar, Sin ta jaddada cewa, tana da ikon mallakar tsibiran Nansha, da yankin teku dake dab da su, wadanda suka hada da tsibirai da sassan tudun ruwa, da yankunan rairayi, ciki har da sashen tudun ruwa na Ren’aijiao.

Wannan batu dai ya biyo bayan yadda bangaren kasar Philippines ya yi ta sabawa alkawarin da ya dauka, ta hanyar yunkurin kafa sashensa na dindindin a kan tsibirai, da sassan tudun ruwa na kasar Sin da babu mutune a kansu, da nufin sace ikon mallakar sashen tudun ruwan Ren’aijiao. Bangaren Sin na ganin Amurka ba ta da nasaba da wannan batu na yankin kudancin tekun kasar Sin, don haka bai kamata ta tsoma baki cikin batun Sin da Philippines ba.

Game da batun jihar Xinjiang da ta Xizang, Wang Wenbin ya jaddada cewa, batun Xinjiang da Xizang, batu ne na cikin gidan kasar Sin. Kaza lika kasar Sin na dora muhimmanci sosai kan kare hakkin dan Adam. Ya ce, jama’ar kasar ne ke da ikon bayyana ra’ayinsu kan kare hakkin dan Adam na kasarsu.

A daya bangaren, kasar Sin tana fatan yin mu’amala tare da Amurka, kan batun kare hakkin dan Adam bisa tushen girmama juna, sai dai Sin din ba za ta amince da duk wani nau’in aiki na tsoma baki cikin harkokin cikin gidanta bisa hujjar kare hakkin dan Adam ba. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha&Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Next Post

Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

Related

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

1 hour ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

3 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

21 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

22 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

23 hours ago
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

1 day ago
Next Post
Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.