ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Da Joe Biden Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden a jiya Talata ta wayar tarho, bisa bukatar shugaba Biden. Shugabannin biyu sun yi tattaunawa mai zurfi da musayar ra’ayi kan dangantakar kasashensu da batutuwan da ke jan hankulansu.

Shugaba Xi ya bayyana cewa, ganawarsa da shugaba Biden a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, ya bude wata mahangar makomarsu. Ya ce cikin watannin da suka gabata, jami’an kasashen biyu sun aiwatar da matsayar da suka cimma sahihanci. Kuma dangantakar Sin da Amurka ta fara daidaituwa, sannan al’ummomin kasashen biyu da ma na kasa da kasa na maraba da hakan. Ya ce a daya bangaren, abubuwan dake yin mummunan tasiri kan dangantakarsu na karuwa, don haka akwai bukatar bangarorin biyu su mayar da hankali kan su.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Fadada Yankunan Tudu Na Teku Da Take Iko Da Su
  • Sin Ta Mai Da Martani Ga Yadda Amurka Ta Gyara Matakin Kayyade Fitar Da Kayayyakin Sassan Laturoni Zuwa Ketare

Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, batun Taiwan shi ne iyaka ta farko da bai kamata a tsallake ba a dangantakar kasashen biyu. Ya ce kasar Sin ba za ta nade hannu tana kallon ayyukan ‘yan aware masu neman ‘yancin yankin da tallafi da goyon bayan da ake ba su daga waje ba.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, shugaba Biden ya ce dangatakar Sin da Amurka ita ce mafi tasiri a duniya. Kuma ci gaban dangantakar da aka samu bayan ganawarsu ta San Francisco, ya nuna cewa bangarorin biyu za su iya inganta hadin gwiwarsu tare da hakuri da bambance-bambancen dake akwai tsakaninsu.

Joe Biden ya kuma nanata cewa, Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi ba ya nufin yi wa Sin taron dangi. Kazalika, Amurka ba ta goyon bayan ‘yancin yankin Taiwan, kuma ba ta neman tada rikici tsakaninta da Sin. Bugu da kari, ya ce Amurka tana goyon bayan manufar Sin daya tak a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya yi karin haske a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau, game da tattaunawa ta wayar tarho, tsakanin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, kan batutuwan sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, da yankin Hong Kong, da jihar Xinjiang, da ta Xizang da sauransu.

Game da batun sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, Wang Wenbin ya bayyana cewa, a yayin tattaunawar, Sin ta jaddada cewa, tana da ikon mallakar tsibiran Nansha, da yankin teku dake dab da su, wadanda suka hada da tsibirai da sassan tudun ruwa, da yankunan rairayi, ciki har da sashen tudun ruwa na Ren’aijiao.

Wannan batu dai ya biyo bayan yadda bangaren kasar Philippines ya yi ta sabawa alkawarin da ya dauka, ta hanyar yunkurin kafa sashensa na dindindin a kan tsibirai, da sassan tudun ruwa na kasar Sin da babu mutune a kansu, da nufin sace ikon mallakar sashen tudun ruwan Ren’aijiao. Bangaren Sin na ganin Amurka ba ta da nasaba da wannan batu na yankin kudancin tekun kasar Sin, don haka bai kamata ta tsoma baki cikin batun Sin da Philippines ba.

Game da batun jihar Xinjiang da ta Xizang, Wang Wenbin ya jaddada cewa, batun Xinjiang da Xizang, batu ne na cikin gidan kasar Sin. Kaza lika kasar Sin na dora muhimmanci sosai kan kare hakkin dan Adam. Ya ce, jama’ar kasar ne ke da ikon bayyana ra’ayinsu kan kare hakkin dan Adam na kasarsu.

A daya bangaren, kasar Sin tana fatan yin mu’amala tare da Amurka, kan batun kare hakkin dan Adam bisa tushen girmama juna, sai dai Sin din ba za ta amince da duk wani nau’in aiki na tsoma baki cikin harkokin cikin gidanta bisa hujjar kare hakkin dan Adam ba. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha&Zainab Zhang)

Xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.