Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane 61 a kauyen Budah Hausa da ke karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna makonni uku da suka gabata sun kashe biyar daga cikin wadanda suka sace.
Mutum 51 da aka sako, an rahoto cewa, sun shaki iskar ‘yanci ne a ranar Talata bayan biyan kudin fansa, da kuma tarin kwayoyi da babura da barayin suka nema.
- Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Kwamitocin Bincike Kan Karkatar Da Kadarorin Gwamnati Da Rikicin Siyasa A Jihar
- Fintiri Ya Nada Farfesa Gidado Da Wasu 4 Hukumar Gudanarwar Jami’ar Adamawa
‘Yan Bindigar sun kuma ci gaba da tsare Biyar daga cikin wadanda suka sacen, acewarsu, kudin fansar ya yi kadan, sai an karo kafin su sako su.
Wani jami’in ‘yan banga a yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar wa manema labarai sakin nasu a ranar Alhamis, inda ya ce, dukkan mutanen biyar din da aka kashe maza ne.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp