• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta yanke shawarar haramta zirga-zirga daga karfe 7:00 na dare zuwa karfe 6:00 na safe a kan iyakokin jihar da makwaftanta, Jihohin Katsina da Sakkwato.

Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu na Jihar, Manir Haidar ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Gusau ranar Talata.
Haidara ya ce an yanke wannan shawarar ne a yayin taron kwamitin tsaro na jihar.

  • Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano
  • Jihar Zamfara Ta Haramta Zirga-zirga A Tsakanin Iyakokinta Da Katsina Da Sokoto Daga Karfe 7 Na Yamma

Ya ce, “Ya zuwa yau (ranar Talata), gwamnatin jihar ta ba da umarnin hana zirga-zirga a kan iyakar Yankara da Jihar Zamfara da Jihar Katsina da kuma kan iyakar Bimasa Zamfara da Jihar Sokoto daga karfe 7:00 na safe. zuwa 6:00 na safe kullum.

“An yi hakan ne don magance matsalar sace-sacen matafiya a kan babbar hanyar Sakkwato zuwa Gusau-Funtua.”

“Wannan wani bangare ne na matakan da gwamnatin jihar ke dauka na ragewa tare da magance ayyukan sace-sacen da ‘yan bindiga ke yi, musamman a manyan titunan jihar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

A cewar kwamishinan, an umurci dukkan masu ababen hawa da matafiya da su bi umarnin gwamnati.

“An umurci hukumomin tsaro da su sanya ido kan iyakokin biyu tare da tabbatar da cikakkiyar kulawa,” in ji shi.

…’Yan Bindiga Sun Sace Masu Sallar Tahajjud

A wani labarin kuma, a daren Litinin din da ta gabata, wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci da ke Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da wasu masu ibada a lokacin da suke Sallar Tahajjud.

Sallar Tahajjud ibada ce da aka saba gudanarwa a cikin kwanaki 10 na karshen watan Ramadan gabanin ranar karamar sallah.

A cewar wani mazaunin unguwar mai suna Mannir wanda ya zanta da LEADERSHIP, maharan sun far wa masallacin ne a lokacin da ake Sallar dare.

Mannir, ya bayyana rashin tabbas game da ainihin adadin mutanen da aka kama.
Mannir ya kara da cewa “Yayin da har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda aka sace ba, hukumomi na ci gaba da bibiyar maharan.”

Har ya zuwa lokacin da aka fitar da wannan rahoto, babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai wannan kazamin hari, lamarin da ya kara janyo rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

Wannan harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fargabar karuwar ta’addanci da ayyukan ta’addanci a Jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, a mako guda da ya gabata ne Gwamna Dauda Lawal ya tattauna da Shugaban Kasa Bola Tinubu domin shawo kan matsalolin tsaro da ke kara kamari a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version