ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta yanke shawarar haramta zirga-zirga daga karfe 7:00 na dare zuwa karfe 6:00 na safe a kan iyakokin jihar da makwaftanta, Jihohin Katsina da Sakkwato.

Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu na Jihar, Manir Haidar ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Gusau ranar Talata.
Haidara ya ce an yanke wannan shawarar ne a yayin taron kwamitin tsaro na jihar.

  • Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano
  • Jihar Zamfara Ta Haramta Zirga-zirga A Tsakanin Iyakokinta Da Katsina Da Sokoto Daga Karfe 7 Na Yamma

Ya ce, “Ya zuwa yau (ranar Talata), gwamnatin jihar ta ba da umarnin hana zirga-zirga a kan iyakar Yankara da Jihar Zamfara da Jihar Katsina da kuma kan iyakar Bimasa Zamfara da Jihar Sokoto daga karfe 7:00 na safe. zuwa 6:00 na safe kullum.

ADVERTISEMENT

“An yi hakan ne don magance matsalar sace-sacen matafiya a kan babbar hanyar Sakkwato zuwa Gusau-Funtua.”

“Wannan wani bangare ne na matakan da gwamnatin jihar ke dauka na ragewa tare da magance ayyukan sace-sacen da ‘yan bindiga ke yi, musamman a manyan titunan jihar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

A cewar kwamishinan, an umurci dukkan masu ababen hawa da matafiya da su bi umarnin gwamnati.

“An umurci hukumomin tsaro da su sanya ido kan iyakokin biyu tare da tabbatar da cikakkiyar kulawa,” in ji shi.

…’Yan Bindiga Sun Sace Masu Sallar Tahajjud

A wani labarin kuma, a daren Litinin din da ta gabata, wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci da ke Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da wasu masu ibada a lokacin da suke Sallar Tahajjud.

Sallar Tahajjud ibada ce da aka saba gudanarwa a cikin kwanaki 10 na karshen watan Ramadan gabanin ranar karamar sallah.

A cewar wani mazaunin unguwar mai suna Mannir wanda ya zanta da LEADERSHIP, maharan sun far wa masallacin ne a lokacin da ake Sallar dare.

Mannir, ya bayyana rashin tabbas game da ainihin adadin mutanen da aka kama.
Mannir ya kara da cewa “Yayin da har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda aka sace ba, hukumomi na ci gaba da bibiyar maharan.”

Har ya zuwa lokacin da aka fitar da wannan rahoto, babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai wannan kazamin hari, lamarin da ya kara janyo rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

Wannan harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fargabar karuwar ta’addanci da ayyukan ta’addanci a Jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, a mako guda da ya gabata ne Gwamna Dauda Lawal ya tattauna da Shugaban Kasa Bola Tinubu domin shawo kan matsalolin tsaro da ke kara kamari a jihar.

Zamfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.