• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakataccen Malamin Kwaleji Ya Dawo Karen Mota A Ribas

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Dakataccen Malamin Kwaleji Ya Dawo Karen Mota A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakataccen Malamin Kwalejin Kimiyya da fasaha ta Captain Elechi Amadi Polytechnic da ke Fatakwal a jihar Ribas, Mista Zoe Solomon Tamunotonye, ya koma karen mota domin neman taro da sisin da zai ciyar da kansa biyo bayan kin biyansa albashinsa na sama da watanni shida da Kwalejin ta ki yi.

A wani faifan bindiyo da aka yada a kafafen sada zumunta, an ga Tamunotonye na gwagwarmayar neman fasinjoji da su shiga motar kabu-kabu a kan hanyar Ikwerre da ke garin Fatakwal babban birnin jihar Ribas.

  • Lalata Da ‘Yar Shekara 14: Kotu Ta Daure Jarumin Nollywood Baba Ijesha Shekara 16 A Gidan Yari

Shi dai malamin kwalejin, hukumar gudanarwar ta Kwalejin ce ta dakatar da shi biyo bayan rahoton da kwamitin da aka kafa domin bincikensa kan zargin lalata da wata dalibar Kwalejin.

Tirka-tirkar alakar da ke tsakaninsa da dalibar har sai da ta kai ga ‘yan sanda sun tsare ita dalibar a caji ofis din Sani Abacha da ke garin na Fatakwal.

Malamin ya dawo ya zargi dalibar da karkatar da kudin da ya kai naira N250,000 da ya bata domin yin kasuwanci kuma ta rike masa makullin ofis da wasu kadarorinsa.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Daga baya ne kuma kwamishinan ‘yan sanda Eboka Friday ya shiga cikin lamarin da har aka sake dalibar bisa cewa bayan da ya saurari dukkanin bangarorin da abun ya shafa, ya gano zargin da malamin ke yi babu sahihin gaskiya a ciki.

Idan za a iya tunawa dai Kwalejin ta Captain Elechi Amadi Polytechnic a watan Maris na 2022 ta fitar da sanarwar na cewa ta samu Zoe Solomon Tamunotonye dumu-dumu kan zarginsa da ake yi da rashin da’a gami da cin zarafin dalibar.

Sanarwar wacce Rijistan Kwalejin Chris Woke ya sanya wa hannu inda suka bai wa malamin Kwalejin zuwa ranar 31 ga watan Mayun 2022 da ya rubuta wasikar neman afuwa da yafiyar Kwalejin tare da daukan alkawarin zai zama daga cikin malamai masu cikakken da’a da ladabi.

Sai dai Malamin ( Zoe Solomon) ya ki rubuta neman yafiyar bisa nashi ra’ayin na cewa shi fa atafau bai aikata laifin komai da zai sanya shi rubuta ban hakuri da neman gafara ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ba Da Gudummawar Dala Miliyan 50 Ga Asusun Yaki Da Annoba Na Bankin Duniya

Next Post

Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 hours ago
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

7 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

9 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

10 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

11 hours ago
Next Post
Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.