• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, nan ba da jimawa ba, za ta yi karin haske game da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka a kasar Sin. 

Kakakin ma’aikatar Wang Wenbin ne ya bayyana haka a yau, yayin taron manema labarai da aka saba yi a kullum, bayan an nemi jin ta bakinsa game da tsokacin da sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya yi yayin ziyararsa a Shanghai. Wang Wenbin ya bayyana cewa, sun riga sun gabatar da makasudin ziyarar jami’in na Amurka, kwanaki biyun da suka gabata, tare kuma da bayyana matsayin kasar Sin kan batun.

  • Xi Ya Yi Kira Ga Chongqing Da Ya Rubuta Nasa Tarihi Cikin Aikin Zamanantar Da Kasar Sin
  • Kasar Sin Ta Bayyana Tarin Rarar Da Take Da Shi Ta Albarkartun Mai Da Iskar Gas

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin ta kasance mai aiwatar da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya bisa ka’idojin kasuwa, haka kuma ta kasance mai nacewa ga tsarin cinikayya tsakanin bangarori da dama da kuma aiwatar da ka’idojin hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) yadda ya kamata. A cewarsa, ana fata bangaren Amurka zai martaba ka’idojin takara bisa adalci da biyayya ga ka’idojin WTO da hada hannu da kasar Sin wajen samar da kyakkyawan yanayin raya dangantakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu cikin aminci.

Har ila yau, Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da tallafi mai yawa na yaki da cutar cizon sauro ta Malaria ga kasa da kasa, ta hanyar amfani da maganin Artemisinin wajen samar da magunguna da tallafin kwararru da ginin cibiyoyin yaki da cutar da horar da jami’ai. Ya ce, a nahiyar Afrika, shirye-shiryen yaki da cutar da magunguna da dabarun kasar Sin, sun samar da fatan rayuwa ga mutanen nahiyar da dake fama da cutar. Ya kara da cewa, kasar Sin na dogaro da cibiyar bincike da horo kan kawar da cutar Malaria ta MDD, wajen horar da sama da jami’an lafiya da masana 2,000 daga kasashe da yankuna 85, game da kandagarki da takaita cutar Malaria da sauran cututtuka masu yaduwa. A cewar hukumar lafiya ta duniya (WHO), kimanin mutane miliyan 240 a yankin kudu da hamadar Sahara kadai, sun amfana da hadin maganin Artemisinin.

Haka zalika, Wang Wenbin, ya ce ci gaba da yaki a Gaza, abu ne da ba za a lamunta ba, kuma kisan gillar da ake wa yara da mata, abu ne da ba za a yi hakuri da shi ba, haka kuma ba za a taba amincewa da kawo tsaiko ga yunkurin Kwamitin Sulhu na MDD na ingiza tsagaita bude wuta ba. Kasar Sin na bukatar kasashe masu ruwa da tsaki, su daina kawo tsaiko kan matakan Kwamitin Sulhun, tare da kira ga bangarorin da batun ya shafa su aiwatar da kudurin Kwamitin Sulhun mai lamba 2728, da cimma tsagaita bude wuta mai dorewa nan take kuma ba tare da gindaya sharadi ba. Bugu da kari a tabbatar da samar da agajin jin kai mai dorewa ba tare da katsewa ba, domin kawo karshen wahalhalun da al’ummar Palasdinu ke fuskanta da daina kunyata wayewar kan bil Adama. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Related

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

6 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

8 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

18 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

20 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

21 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

23 hours ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.