ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Ran 24 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya fara ziyarar aiki a kasar Sin, karo na biyu a wa’adin aikinsa. Bisa labarin da kafofin yada labarai na Amurka suka bayar, an ce, Blinken zai ci gaba da shafawa kasar Sin bakin fenti kamar yadda sakatariyar baitul malin kasar Janet L. Yellen ta yi, kan wasu bangarorin da Sin take da fifiko sama da Amurka, da cewa wai “Yawan kayayyakin da masana’antun Sin ke samarwa ya wuce kima”. Amma ko da gaske ne yawan kayayyakin da Sin ta samar ya wuce misali, ko yawan damuwar Amurka ya wuce kima?

Bari mu duba wasu alkaluma. Hukumar kula da makamashi ta duniya wato IEA ta yi kiyasin cewa, domin cimma burin samun daidaito tsakanin yawan hayaki mai dumama yanayi da za a fitar da yawan abubuwan da za su shawo kan hayakin, zuwa shekara ta 2030, za a bukaci motoci masu amfani da makamashi mai tsabta kimanin miliyan 45, yayin da za a bukaci wutar lantarkin da yawansa ya kai gigawatt 820 daga sabbin injunan samar da wutar lantarki masu amfani da hasken rana. Wadannan alkaluma sun ninka sau 4.5 da 4 bisa na shekarar 2022. A matsayin kasa mafi karfi a fannin samarwa da sayar da motoci masu amfani da makamashi mai tsabta, kasar Sin ta samar da motocin da yawansu ya kai fiye da miliyan 9.5 a bara, kuma ta fitar da kimanin miliyan 1.2 ketare. Wato adadin da ya kai kusan kashi 90% na biyan bukatun cikin gidan kasar ta Sin. Abin da ya bayyana cewa, karancin samar da hajoji masu alaka da makamashi mai tsabta matsala ce da duniya ke fuskanta, a maimakon a ce an samar da su fiye da kima. Kasashen duniya na matukar bukatar nagartaccen karfin samar da hajojin da Sin take da shi.

Damuwa da rashin kwarin gwiwa da Amurka ke da su na tilasta mata daukar matakan shafawa kasar Sin bakin fenti kan sana’o’inta da ke da fifiko, don mai da su barazanar da za ta sanya sauran kasashe fargaba. Amma, ba za a iya mai da baki fari ba, mataki daya tilo da Amurka za ta dauka wajen rage damuwarta ita ce, ta kara karfin kirkire-kirkire da hadin kai don more ci gaba tare. Kamata ya yi Amurka ta mai da hankali kan kyautata kwarewarta, a maimakon gurbata gaskiya da shafawa wasu bakin fenti, tana cewa wai hajoji masu nasaba da makamashi mai tsabta da Sin ta samar na dogaro da rangwamen da gwamnatin Sin ke bayarwa, wanda ya illata kasuwarta. To, kara karfin takara ba shi da alaka da magana ko furucin da aka yi, ya dogara ne da nagartaccen matakin da za a dauka. (Mai zana da rubuta: MINA)

ADVERTISEMENT
Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.