• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Sayar Da Kamfanonin Samar Da Wuta 4

by Bello Hamza
2 years ago
TCN

A halin yanzu gwamnatin tarayya da bayar da umarnin sake sayar da wasu kamfanonin samar da wutar lantarki 4 ta kuma umarci a sake rarraba wasu kamfanonin zuwa kananan kamfanoni saboda girmansu ya na kawo cikas ga yadda suke gudanar da ayyukansu.

Sanarwar ta kuma ce gwamnati ba za ta janye sayar da kamfanonin da ta yi ba amma za a sake rarraba su don su samu yin aiki yadda ya kamata, al’umma su amfana da ayyukansu ba kamar yadda lamarin yake a halin yanzu ba.

  • Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani
  • Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo

Wannan kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin a sayar da wasu kamfanoni samar da wutar lantarki 4 (Discos) wadanda bankuna da kamfanin AMCON suka karbe ragamar tafiyar da su saboda basuka.

Bankin UBA ne ta karbe harkokin kamfanin samar da wuta na Abuja yayin da bankin Fidelity Bank ya karbe harkokin kamfanin samar da wuta na Benin da Kaduna da na Kano. Sai kuma kamfanin samar da wuta na Ibadan da ya koma karkashin kamfanin AMCON. An yanke wa wadannan kamfannnin hukuncin ne saboda sun kasa biyan kudaden da wadannan bankuna ke binsu.

Gwamnati ta bayyana cewa, wadanda suka sayi kamfanonin a lokacin da aka yi gwanjon su ne tunda farko a shekarar 2013 ne basu da kudi da kuma kwarewar da ake bukata na tafiyar da kamfanoni irin wannan.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Wannan ma yana zuwa ne a yayin da majalisar dattawa ta caccaki kamfanonin Discos a kan rashin iya aiki tun da aka sayar musu da kamfanonin a shekara 10 da suka wuce.

A jawabinsa a yayin da ‘yan kwamitin majalisar dattawa a kan wutar lantarki a karkashin jagorancin Sanata Eyinnaya Abaribe, suka kai masa ziyara, Ministan wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa, a halin yanzu gwamnatin tarayya ta fara aikin sake fasalin kamfanonin samar da wuta 11 na kasar nan.

Ya ce, akwai ayyyuka fiye da 100 da kamfanonin suka bayar amma fiye da shekara 23 da suka wuce amma har yanzu ba a kammala ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Fashewar Bututun Iskar Gas Na Nord Stream Karkashin Jagorancin MDD

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Fashewar Bututun Iskar Gas Na Nord Stream Karkashin Jagorancin MDD

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.