ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
EFCC

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba a tsakanin tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello da Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Zamba ta EFCC, inda shugaban hukumar, Ola Olukoyede ya yi barazanar cewa zai yi murabus matukar ba a hukunta tsohon gwamnan ba.

Mista Ola ya fadi hakan ne a wani taron manema labarai a shalkwatar EFCC da ke Abuja, a ranar Talata tare da jaddada cewa hatta wadanda suka bai wa Yahaya Bello mafaka su ma za su fuskanci fushin doka.

  • Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha
  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata

A farkon makon nan, tsohon gwamnan, Yahaya Bello ya bayyana cewa a shirye yake ya gurfana a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja domin amsa tambayoyi kan tuhume-tuhumen da hukumar kula da cin hanci da rashawa (EFCC) take yi masa har guda 19, amma yana tsoron ya fito ne a cafke shi.

ADVERTISEMENT

Yahaya Bello bai gurfana a gaban kotu na zaman shari’ar ba a ranar Talata, ya yi magana ne ta bakin tawagar lauyoyinsa a madadinsa.

Daya daga cikin tawagar lauyoyinsa, Mista Adeola Adedipe ya bayyana wa alkali cewa wanda yake karewa baya tsoron gurfana a gaban kotu, amma yana mutukar tsoron a kama shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Wanda ake uhuma yana son zuwa kotu, amma yana tsoron umurnin da aka bayar da kama sh,” in ji Adedipe.

Saboda haka, ya bukaci kotu ta janye umurnin kama da aka bayar tun da farko. Adedipe ce kamar yadda aka bayar da umurnin a kama shi, hakan ya saba wa doka na kare wanda ake tuhuma.

Ya ce a lokacin wannan zaman shari’ar na ranar Talata ne kadai kotu ta amince a mika karar da ake wa wanda ake tuhuma wurin lauyansa domin kare shi.

Sai dai kuma tsahon gwammann ya yi ikirarin cewa EFCC haramtacciyar hukuma ce.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ba ta shawarci dukkan jihohi 36 da ke kasarr nan kafin kafa dokokin EFCC ba ta hanyar majalisar kasa.

Ya ce sashi na 12 na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, ya bukaci majalisun dokoki da ke jihohi su amince da wani doka kafin a fara aiwatarwa.

“Wannan batu yana da matukar muhimmanci game da tsarin mulkin kasa da dokokin tarayya. Ya kamata a warware shi kafin EFCC ta zama halartacciyar hukuma,” in ji lauyan Yahaya Bello.

Sai dai kuma lauyan Hukumar EFCC, Mista Kemi Pinheiro, ya bukaci kotu a kan karta amince da bukatar lauya mai kare wanda ake tuhuma. Ya ce bai kamata a kyale batun kama shi ba har sai wanda ake kara ya mika kansa a gaban kuliya.

Lauyan EFCC ya kara da cewa sashe na 396 na dokar kasar nan ya tanadi cewa, kotu ba ta da hurumin amsar duk wani bukata na wanda ake kara har sai ya mika kansa a gaban kotu.

Ya ce hukumar ba za ta janye batun kama shi ba har sai wanda ake tuhuma ya mika kansa a zama na gaba da kotun za ta yi. Ya ce tuhumar da ake masa ba ta da alaka da jiha ko majalisa, tuhuma ce a tsakanin wani mtum ake yi masa zargin yin almundahana da kudaden jama’a.

 

EFCC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.