• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yahaya Bello Ya Ba Ma’aikata Hutu Saboda Buhari Zai Kai Ziyar Bude Wasu Ayyuka A Jihar Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba a tsakanin tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello da Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Zamba ta EFCC, inda shugaban hukumar, Ola Olukoyede ya yi barazanar cewa zai yi murabus matukar ba a hukunta tsohon gwamnan ba.

Mista Ola ya fadi hakan ne a wani taron manema labarai a shalkwatar EFCC da ke Abuja, a ranar Talata tare da jaddada cewa hatta wadanda suka bai wa Yahaya Bello mafaka su ma za su fuskanci fushin doka.

  • Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha
  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata

A farkon makon nan, tsohon gwamnan, Yahaya Bello ya bayyana cewa a shirye yake ya gurfana a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja domin amsa tambayoyi kan tuhume-tuhumen da hukumar kula da cin hanci da rashawa (EFCC) take yi masa har guda 19, amma yana tsoron ya fito ne a cafke shi.

Yahaya Bello bai gurfana a gaban kotu na zaman shari’ar ba a ranar Talata, ya yi magana ne ta bakin tawagar lauyoyinsa a madadinsa.

Daya daga cikin tawagar lauyoyinsa, Mista Adeola Adedipe ya bayyana wa alkali cewa wanda yake karewa baya tsoron gurfana a gaban kotu, amma yana mutukar tsoron a kama shi.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

“Wanda ake uhuma yana son zuwa kotu, amma yana tsoron umurnin da aka bayar da kama sh,” in ji Adedipe.

Saboda haka, ya bukaci kotu ta janye umurnin kama da aka bayar tun da farko. Adedipe ce kamar yadda aka bayar da umurnin a kama shi, hakan ya saba wa doka na kare wanda ake tuhuma.

Ya ce a lokacin wannan zaman shari’ar na ranar Talata ne kadai kotu ta amince a mika karar da ake wa wanda ake tuhuma wurin lauyansa domin kare shi.

Sai dai kuma tsahon gwammann ya yi ikirarin cewa EFCC haramtacciyar hukuma ce.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ba ta shawarci dukkan jihohi 36 da ke kasarr nan kafin kafa dokokin EFCC ba ta hanyar majalisar kasa.

Ya ce sashi na 12 na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, ya bukaci majalisun dokoki da ke jihohi su amince da wani doka kafin a fara aiwatarwa.

“Wannan batu yana da matukar muhimmanci game da tsarin mulkin kasa da dokokin tarayya. Ya kamata a warware shi kafin EFCC ta zama halartacciyar hukuma,” in ji lauyan Yahaya Bello.

Sai dai kuma lauyan Hukumar EFCC, Mista Kemi Pinheiro, ya bukaci kotu a kan karta amince da bukatar lauya mai kare wanda ake tuhuma. Ya ce bai kamata a kyale batun kama shi ba har sai wanda ake kara ya mika kansa a gaban kuliya.

Lauyan EFCC ya kara da cewa sashe na 396 na dokar kasar nan ya tanadi cewa, kotu ba ta da hurumin amsar duk wani bukata na wanda ake kara har sai ya mika kansa a gaban kotu.

Ya ce hukumar ba za ta janye batun kama shi ba har sai wanda ake tuhuma ya mika kansa a zama na gaba da kotun za ta yi. Ya ce tuhumar da ake masa ba ta da alaka da jiha ko majalisa, tuhuma ce a tsakanin wani mtum ake yi masa zargin yin almundahana da kudaden jama’a.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha

Next Post

Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

5 hours ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

15 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

16 hours ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.