ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Tataburzar EFCC Da Yahaya Bello Na Daukar Sabon Salo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
EFCC

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba a tsakanin tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello da Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Zamba ta EFCC, inda shugaban hukumar, Ola Olukoyede ya yi barazanar cewa zai yi murabus matukar ba a hukunta tsohon gwamnan ba.

Mista Ola ya fadi hakan ne a wani taron manema labarai a shalkwatar EFCC da ke Abuja, a ranar Talata tare da jaddada cewa hatta wadanda suka bai wa Yahaya Bello mafaka su ma za su fuskanci fushin doka.

  • Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha
  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata

A farkon makon nan, tsohon gwamnan, Yahaya Bello ya bayyana cewa a shirye yake ya gurfana a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja domin amsa tambayoyi kan tuhume-tuhumen da hukumar kula da cin hanci da rashawa (EFCC) take yi masa har guda 19, amma yana tsoron ya fito ne a cafke shi.

ADVERTISEMENT

Yahaya Bello bai gurfana a gaban kotu na zaman shari’ar ba a ranar Talata, ya yi magana ne ta bakin tawagar lauyoyinsa a madadinsa.

Daya daga cikin tawagar lauyoyinsa, Mista Adeola Adedipe ya bayyana wa alkali cewa wanda yake karewa baya tsoron gurfana a gaban kotu, amma yana mutukar tsoron a kama shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Wanda ake uhuma yana son zuwa kotu, amma yana tsoron umurnin da aka bayar da kama sh,” in ji Adedipe.

Saboda haka, ya bukaci kotu ta janye umurnin kama da aka bayar tun da farko. Adedipe ce kamar yadda aka bayar da umurnin a kama shi, hakan ya saba wa doka na kare wanda ake tuhuma.

Ya ce a lokacin wannan zaman shari’ar na ranar Talata ne kadai kotu ta amince a mika karar da ake wa wanda ake tuhuma wurin lauyansa domin kare shi.

Sai dai kuma tsahon gwammann ya yi ikirarin cewa EFCC haramtacciyar hukuma ce.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ba ta shawarci dukkan jihohi 36 da ke kasarr nan kafin kafa dokokin EFCC ba ta hanyar majalisar kasa.

Ya ce sashi na 12 na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, ya bukaci majalisun dokoki da ke jihohi su amince da wani doka kafin a fara aiwatarwa.

“Wannan batu yana da matukar muhimmanci game da tsarin mulkin kasa da dokokin tarayya. Ya kamata a warware shi kafin EFCC ta zama halartacciyar hukuma,” in ji lauyan Yahaya Bello.

Sai dai kuma lauyan Hukumar EFCC, Mista Kemi Pinheiro, ya bukaci kotu a kan karta amince da bukatar lauya mai kare wanda ake tuhuma. Ya ce bai kamata a kyale batun kama shi ba har sai wanda ake kara ya mika kansa a gaban kuliya.

Lauyan EFCC ya kara da cewa sashe na 396 na dokar kasar nan ya tanadi cewa, kotu ba ta da hurumin amsar duk wani bukata na wanda ake kara har sai ya mika kansa a gaban kotu.

Ya ce hukumar ba za ta janye batun kama shi ba har sai wanda ake tuhuma ya mika kansa a zama na gaba da kotun za ta yi. Ya ce tuhumar da ake masa ba ta da alaka da jiha ko majalisa, tuhuma ce a tsakanin wani mtum ake yi masa zargin yin almundahana da kudaden jama’a.

 

EFCC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

EFCC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.