• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki

by Zubairu M Lawal
1 year ago
Wutar Lantarki

Majalisar dokokin Jihar Nasarawa ta bai wa kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distrust Company, wa’adin makonni biyu ya gyara matsalar wuta da ake fuskanta a jihar ko kuma ya bar jihar.

Kakakin Majalisan Dokokin jihar Hon. Danladi Jatau tare da mambobinsa suka bayyana haka a ranar Talata, okacin tattaunawa da Shugabannin Kamfanin Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) a zauren majalisar.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Kakakin majalisar, Hon. Danladi Jatau ne ya jagoranci zaman.

Bayan wakilan Kamfanin AEDC da NAEPA sun gurfana gaban majalisan.

Kakakin majalisar ya bukaci jagorarorin su bayyana a gaban mambobin matsalisar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

“sunana Injiniya Jonathan Adeyemi shugaban sashen kasuwanci da ke wakiltar Jihar Kogi, Neja da Jihar Nasarawa a kamfanin AEDC”.

Shi ma shugaban Nasarawa State Electricity Power Agency, (NAEPA ), Injiniya Suleiman Umar ya gabatar da kansa.

Majalisar ta gudanar da tambayoyi kan dalilin rashin samun wutan lantarki ga al’umman jihar masamman bangaren talakawan jihar.

Sannan ta bukaci da su bayyana mata adadin kwastomomin da ke amfani da lantarki a jihar.

Da adadin mita da ake amfani da kati da AEDC ta samar a fadin jihar.

Ta kuma bayyana kudin da ta samu daga watan daya zuwa watanni hudu na wannan shekarar.

Sannan ta bayyana yawan injinan rarraba wutar da ke unguwanni a fadin jihar.

Ta kuma bayyana karfin wutar da ta ke samarwa ga al’umman jihar.

Haka zalika ta bayyana dalilan da ya sa ba a samun isasshiyar wutar lantarki a Lafia, babban birnin jihar.

Majalisar ta bukaci shugaban samar da karfin hasken wutan lantarki ta jihar, Injiniya Sulaiman Umar, ya gaggauta kawo karshen aikin wutan lantarki a karamar hukumar Toto da yankin Umasha da kauyukan da ke kusa da yankin tun da Gwamna Abdullahi Sule ya mika makudan kudade domin samar da wutan lantarki.

‘Yan majalisar sun nuna rashin amincewarsu da tsarin da kamfanin AEDC ya ce yana yi na raba wutan lantarki kashi hudu.

Kamar yadda kamfanin ya bayyana cewa akwai sashen da ke samun wutar awa 20 da masu samun awa 16 da masu samun awa takwas da masu samun awa hudh.

Majalisar ta ce tun da kasuwanci suke yi kuma suna samun riba babu dalilin da zai bambamce masu amfanin da wutar.

Sannan majalisar ta gargadin kamfanin AEDC da cewa babu dalilin da idan injin wutan lantarki ko waya ta samu matsala a ce al’ummar unguwar ne za su hada kudi su gyara alhalin suna biyan kudin wuta.

Majalisar ta ce ba zai yiwu ba tun da al’umma na biyan kudin wuta bai kamata idan wuta ta samu matsala a ce su zasu gyara ba.

Duk da kokarin kare martabar kamfanoninsu, inda suka yi dogayen bayanai tare da amsa tambayoyi, kamfanin AEDC da NAEPA ba su gamsar da ‘yan majalisar ba.

Daga bisani majalisar ta ba su makonnj biyu da su gaggauta warware matsalar ko su sanya kafar wando daya da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra
Labarai

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
Next Post
Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.