ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki

by Zubairu M Lawal
2 years ago
Wutar Lantarki

Majalisar dokokin Jihar Nasarawa ta bai wa kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distrust Company, wa’adin makonni biyu ya gyara matsalar wuta da ake fuskanta a jihar ko kuma ya bar jihar.

Kakakin Majalisan Dokokin jihar Hon. Danladi Jatau tare da mambobinsa suka bayyana haka a ranar Talata, okacin tattaunawa da Shugabannin Kamfanin Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) a zauren majalisar.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Kakakin majalisar, Hon. Danladi Jatau ne ya jagoranci zaman.

ADVERTISEMENT

Bayan wakilan Kamfanin AEDC da NAEPA sun gurfana gaban majalisan.

Kakakin majalisar ya bukaci jagorarorin su bayyana a gaban mambobin matsalisar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“sunana Injiniya Jonathan Adeyemi shugaban sashen kasuwanci da ke wakiltar Jihar Kogi, Neja da Jihar Nasarawa a kamfanin AEDC”.

Shi ma shugaban Nasarawa State Electricity Power Agency, (NAEPA ), Injiniya Suleiman Umar ya gabatar da kansa.

Majalisar ta gudanar da tambayoyi kan dalilin rashin samun wutan lantarki ga al’umman jihar masamman bangaren talakawan jihar.

Sannan ta bukaci da su bayyana mata adadin kwastomomin da ke amfani da lantarki a jihar.

Da adadin mita da ake amfani da kati da AEDC ta samar a fadin jihar.

Ta kuma bayyana kudin da ta samu daga watan daya zuwa watanni hudu na wannan shekarar.

Sannan ta bayyana yawan injinan rarraba wutar da ke unguwanni a fadin jihar.

Ta kuma bayyana karfin wutar da ta ke samarwa ga al’umman jihar.

Haka zalika ta bayyana dalilan da ya sa ba a samun isasshiyar wutar lantarki a Lafia, babban birnin jihar.

Majalisar ta bukaci shugaban samar da karfin hasken wutan lantarki ta jihar, Injiniya Sulaiman Umar, ya gaggauta kawo karshen aikin wutan lantarki a karamar hukumar Toto da yankin Umasha da kauyukan da ke kusa da yankin tun da Gwamna Abdullahi Sule ya mika makudan kudade domin samar da wutan lantarki.

‘Yan majalisar sun nuna rashin amincewarsu da tsarin da kamfanin AEDC ya ce yana yi na raba wutan lantarki kashi hudu.

Kamar yadda kamfanin ya bayyana cewa akwai sashen da ke samun wutar awa 20 da masu samun awa 16 da masu samun awa takwas da masu samun awa hudh.

Majalisar ta ce tun da kasuwanci suke yi kuma suna samun riba babu dalilin da zai bambamce masu amfanin da wutar.

Sannan majalisar ta gargadin kamfanin AEDC da cewa babu dalilin da idan injin wutan lantarki ko waya ta samu matsala a ce al’ummar unguwar ne za su hada kudi su gyara alhalin suna biyan kudin wuta.

Majalisar ta ce ba zai yiwu ba tun da al’umma na biyan kudin wuta bai kamata idan wuta ta samu matsala a ce su zasu gyara ba.

Duk da kokarin kare martabar kamfanoninsu, inda suka yi dogayen bayanai tare da amsa tambayoyi, kamfanin AEDC da NAEPA ba su gamsar da ‘yan majalisar ba.

Daga bisani majalisar ta ba su makonnj biyu da su gaggauta warware matsalar ko su sanya kafar wando daya da su.

Wutar Lantarki
Zubairu M Lawal
+ postsBio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnati Ta Jibge Jami’an Tsaro Domin Gudanar da Zaɓen Fidda Gwanin APC A Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    ’Yansanda Sun Tabbatar da Sace Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.