• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki

by Zubairu M Lawal
1 year ago
in Labarai
0
Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar dokokin Jihar Nasarawa ta bai wa kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distrust Company, wa’adin makonni biyu ya gyara matsalar wuta da ake fuskanta a jihar ko kuma ya bar jihar.

Kakakin Majalisan Dokokin jihar Hon. Danladi Jatau tare da mambobinsa suka bayyana haka a ranar Talata, okacin tattaunawa da Shugabannin Kamfanin Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) a zauren majalisar.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Kakakin majalisar, Hon. Danladi Jatau ne ya jagoranci zaman.

Bayan wakilan Kamfanin AEDC da NAEPA sun gurfana gaban majalisan.

Kakakin majalisar ya bukaci jagorarorin su bayyana a gaban mambobin matsalisar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

“sunana Injiniya Jonathan Adeyemi shugaban sashen kasuwanci da ke wakiltar Jihar Kogi, Neja da Jihar Nasarawa a kamfanin AEDC”.

Shi ma shugaban Nasarawa State Electricity Power Agency, (NAEPA ), Injiniya Suleiman Umar ya gabatar da kansa.

Majalisar ta gudanar da tambayoyi kan dalilin rashin samun wutan lantarki ga al’umman jihar masamman bangaren talakawan jihar.

Sannan ta bukaci da su bayyana mata adadin kwastomomin da ke amfani da lantarki a jihar.

Da adadin mita da ake amfani da kati da AEDC ta samar a fadin jihar.

Ta kuma bayyana kudin da ta samu daga watan daya zuwa watanni hudu na wannan shekarar.

Sannan ta bayyana yawan injinan rarraba wutar da ke unguwanni a fadin jihar.

Ta kuma bayyana karfin wutar da ta ke samarwa ga al’umman jihar.

Haka zalika ta bayyana dalilan da ya sa ba a samun isasshiyar wutar lantarki a Lafia, babban birnin jihar.

Majalisar ta bukaci shugaban samar da karfin hasken wutan lantarki ta jihar, Injiniya Sulaiman Umar, ya gaggauta kawo karshen aikin wutan lantarki a karamar hukumar Toto da yankin Umasha da kauyukan da ke kusa da yankin tun da Gwamna Abdullahi Sule ya mika makudan kudade domin samar da wutan lantarki.

‘Yan majalisar sun nuna rashin amincewarsu da tsarin da kamfanin AEDC ya ce yana yi na raba wutan lantarki kashi hudu.

Kamar yadda kamfanin ya bayyana cewa akwai sashen da ke samun wutar awa 20 da masu samun awa 16 da masu samun awa takwas da masu samun awa hudh.

Majalisar ta ce tun da kasuwanci suke yi kuma suna samun riba babu dalilin da zai bambamce masu amfanin da wutar.

Sannan majalisar ta gargadin kamfanin AEDC da cewa babu dalilin da idan injin wutan lantarki ko waya ta samu matsala a ce al’ummar unguwar ne za su hada kudi su gyara alhalin suna biyan kudin wuta.

Majalisar ta ce ba zai yiwu ba tun da al’umma na biyan kudin wuta bai kamata idan wuta ta samu matsala a ce su zasu gyara ba.

Duk da kokarin kare martabar kamfanoninsu, inda suka yi dogayen bayanai tare da amsa tambayoyi, kamfanin AEDC da NAEPA ba su gamsar da ‘yan majalisar ba.

Daga bisani majalisar ta ba su makonnj biyu da su gaggauta warware matsalar ko su sanya kafar wando daya da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AEDCMajalisar Dokokin NasarawaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano

Next Post

Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da É—umi-É—uminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.