ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki

by Zubairu M Lawal
2 years ago
Wutar Lantarki

Majalisar dokokin Jihar Nasarawa ta bai wa kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distrust Company, wa’adin makonni biyu ya gyara matsalar wuta da ake fuskanta a jihar ko kuma ya bar jihar.

Kakakin Majalisan Dokokin jihar Hon. Danladi Jatau tare da mambobinsa suka bayyana haka a ranar Talata, okacin tattaunawa da Shugabannin Kamfanin Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) a zauren majalisar.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Kakakin majalisar, Hon. Danladi Jatau ne ya jagoranci zaman.

ADVERTISEMENT

Bayan wakilan Kamfanin AEDC da NAEPA sun gurfana gaban majalisan.

Kakakin majalisar ya bukaci jagorarorin su bayyana a gaban mambobin matsalisar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

“sunana Injiniya Jonathan Adeyemi shugaban sashen kasuwanci da ke wakiltar Jihar Kogi, Neja da Jihar Nasarawa a kamfanin AEDC”.

Shi ma shugaban Nasarawa State Electricity Power Agency, (NAEPA ), Injiniya Suleiman Umar ya gabatar da kansa.

Majalisar ta gudanar da tambayoyi kan dalilin rashin samun wutan lantarki ga al’umman jihar masamman bangaren talakawan jihar.

Sannan ta bukaci da su bayyana mata adadin kwastomomin da ke amfani da lantarki a jihar.

Da adadin mita da ake amfani da kati da AEDC ta samar a fadin jihar.

Ta kuma bayyana kudin da ta samu daga watan daya zuwa watanni hudu na wannan shekarar.

Sannan ta bayyana yawan injinan rarraba wutar da ke unguwanni a fadin jihar.

Ta kuma bayyana karfin wutar da ta ke samarwa ga al’umman jihar.

Haka zalika ta bayyana dalilan da ya sa ba a samun isasshiyar wutar lantarki a Lafia, babban birnin jihar.

Majalisar ta bukaci shugaban samar da karfin hasken wutan lantarki ta jihar, Injiniya Sulaiman Umar, ya gaggauta kawo karshen aikin wutan lantarki a karamar hukumar Toto da yankin Umasha da kauyukan da ke kusa da yankin tun da Gwamna Abdullahi Sule ya mika makudan kudade domin samar da wutan lantarki.

‘Yan majalisar sun nuna rashin amincewarsu da tsarin da kamfanin AEDC ya ce yana yi na raba wutan lantarki kashi hudu.

Kamar yadda kamfanin ya bayyana cewa akwai sashen da ke samun wutar awa 20 da masu samun awa 16 da masu samun awa takwas da masu samun awa hudh.

Majalisar ta ce tun da kasuwanci suke yi kuma suna samun riba babu dalilin da zai bambamce masu amfanin da wutar.

Sannan majalisar ta gargadin kamfanin AEDC da cewa babu dalilin da idan injin wutan lantarki ko waya ta samu matsala a ce al’ummar unguwar ne za su hada kudi su gyara alhalin suna biyan kudin wuta.

Majalisar ta ce ba zai yiwu ba tun da al’umma na biyan kudin wuta bai kamata idan wuta ta samu matsala a ce su zasu gyara ba.

Duk da kokarin kare martabar kamfanoninsu, inda suka yi dogayen bayanai tare da amsa tambayoyi, kamfanin AEDC da NAEPA ba su gamsar da ‘yan majalisar ba.

Daga bisani majalisar ta ba su makonnj biyu da su gaggauta warware matsalar ko su sanya kafar wando daya da su.

Wutar Lantarki
Zubairu M Lawal
+ postsBio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tinubu Ya Ƙaddamar Da Gadar Ƙasa Da Tituna A Akwanga
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnati Ta Jibge Jami’an Tsaro Domin Gudanar da Zaɓen Fidda Gwanin APC A Nasarawa

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

Nijeriya Da Japan Sun Kulla Yarjejeniya Don Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Yankin Sahel

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.