• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Shirin Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya —APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Bashiru ya bayyana cewa babu wani shiri na bayar da Nijeriya karkashin tsarin jam’iyya daya, amma jam’iyyar za ta ci gaba da lashe zabe a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yi wa dimbin magoya bayan jam’iyyar jawabi a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, wanda suka magoya bayan jam’iyyar suka mamaye shalkwatan domin nuna goyon baya ga shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

  • Umarnin Kotu Da Ya Tabbatar Da Dakatar Da Ganduje Bai Inganta Ba, Ba Za Mu Yi Biyayya Ba – APC
  • Garkuwa Da ‘Yan Makaranta: Nijeriya Ba Za Ta Sake Biyan Kuɗin Fansa Ba – Tinubu

Ya ce, “Mu ba mu ce dole sai Nijeriya ta koma tsarin jam’iya daya ba. Amma mun gina jam’iyyar da za ta dunga lashe zabe a ko da yaushe. Muna tabbatar da cewa akwai kudin samar da ilimi da kuma sauran ababen more rayuwa.

“Makiya ba su isa su hana mu ci gaba ba. Muna bayar da goyon baya ga jagoranmu, mai girma Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu bisa yadda yake aiwatar da shirinsa na sake farfado da kasar nan. Muna kara hada kai karkashin jagorancin shugaban jam’iyyarmu na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.”

A kwanan nan dai Ganduje yana fuskantar ce-ce-ku-ce game da dakatar da shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Amma da yake jawabi ga dimbin magoya bayan jam’iyyar, Ganduje ya ce wasu ne kawai suke jin tsoron yadda yake aiwatar da lamuran jam’iyyar, wanda suka kulla masa kutun-gwila.

“Sun jin tsoron yadda muke sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar. Suna jin tsoro ne saboda muna samun mutane wadanda suke yin tururuwa wajen shiga jam’iyyar a ko’ina a fadin kasar nan. Wannan shi ya haddasa musu tsoro a zukatansu.

“Suna sa ido a 2027, amma a wannan lokaci babu wani gurbi. Shugaban kasarmu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ne zai ci gaba da mulkin Nijeriya idan Allah ya yarda.”

Da yake kira ga magoya bayan APC su yi watsi da abun da ya kira dirama, Ganduje ya ce, “Mun fahimci abubuwan da suke yi. Wasan kwaikwayon siyasa ne. Suna yin wannan dirama ne domin su boye gazawarsu. Ba za mu taba barin su ci gaba da wannan ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaAPCsiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida: AMDF Ta Nemi A Bai Wa ‘Yan Jarida Kariya A Afirka

Next Post

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

3 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 month ago
Next Post
Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.