ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Shirin Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya —APC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Bashiru ya bayyana cewa babu wani shiri na bayar da Nijeriya karkashin tsarin jam’iyya daya, amma jam’iyyar za ta ci gaba da lashe zabe a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yi wa dimbin magoya bayan jam’iyyar jawabi a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, wanda suka magoya bayan jam’iyyar suka mamaye shalkwatan domin nuna goyon baya ga shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

  • Umarnin Kotu Da Ya Tabbatar Da Dakatar Da Ganduje Bai Inganta Ba, Ba Za Mu Yi Biyayya Ba – APC
  • Garkuwa Da ‘Yan Makaranta: Nijeriya Ba Za Ta Sake Biyan Kuɗin Fansa Ba – Tinubu

Ya ce, “Mu ba mu ce dole sai Nijeriya ta koma tsarin jam’iya daya ba. Amma mun gina jam’iyyar da za ta dunga lashe zabe a ko da yaushe. Muna tabbatar da cewa akwai kudin samar da ilimi da kuma sauran ababen more rayuwa.

ADVERTISEMENT

“Makiya ba su isa su hana mu ci gaba ba. Muna bayar da goyon baya ga jagoranmu, mai girma Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu bisa yadda yake aiwatar da shirinsa na sake farfado da kasar nan. Muna kara hada kai karkashin jagorancin shugaban jam’iyyarmu na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.”

A kwanan nan dai Ganduje yana fuskantar ce-ce-ku-ce game da dakatar da shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Amma da yake jawabi ga dimbin magoya bayan jam’iyyar, Ganduje ya ce wasu ne kawai suke jin tsoron yadda yake aiwatar da lamuran jam’iyyar, wanda suka kulla masa kutun-gwila.

“Sun jin tsoron yadda muke sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar. Suna jin tsoro ne saboda muna samun mutane wadanda suke yin tururuwa wajen shiga jam’iyyar a ko’ina a fadin kasar nan. Wannan shi ya haddasa musu tsoro a zukatansu.

“Suna sa ido a 2027, amma a wannan lokaci babu wani gurbi. Shugaban kasarmu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ne zai ci gaba da mulkin Nijeriya idan Allah ya yarda.”

Da yake kira ga magoya bayan APC su yi watsi da abun da ya kira dirama, Ganduje ya ce, “Mun fahimci abubuwan da suke yi. Wasan kwaikwayon siyasa ne. Suna yin wannan dirama ne domin su boye gazawarsu. Ba za mu taba barin su ci gaba da wannan ba.”

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.