• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Wallafa Makalar Da Ya Sanyawa Hannu A Jaridar Kasar Serbia

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaba Xi Ya Wallafa Makalar Da Ya Sanyawa Hannu A Jaridar Kasar Serbia
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

A ci gaba da ziyarar aiki da yake yi a wasu kasashen Turai, a yau Talata 7 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya wallafa makalar da ya sanyawa hannu a jaridar Politika ta kasar ta Serbia a jajibirin ya kai ziyararsa ta aiki a Belgrade.

Makalar ta shugaba Xi mai taken “Fatan hasken managarcin kawancen mu zai haskaka tafarkin hadin gwiwar Sin da Serbia”, ta hakaito shugaban na Sin na bayyana cewa, wannan ne karo na biyu da zai kai ziyara a Serbia, kasa mai kyakkyawan muhalli da dogon tarihi, tun bayan da ya kama aiki a matsayin shugaban jamhuriyar jama’ar kasar Sin.

  • Xi Ya Yi Tsokaci Kan Hargitsin Palastinu Da Isra’ila Da Rikicin Ukraine

Ya ce duk da nisan dake tsakanin Sin da Serbia, kawancen dake tsakanin kasashen biyu na kara karfafa a tsawon lokaci, wanda hakan ya samar da wani kyakkyawan misali na musaya tsakanin kasashen da al’ummunsu. Kaza lika ya jaddada cewa, ta hanyar wannan ziyara, yana fatan yin aiki tare da bangaren Serbia, wajen ci gaba da yaukaka managarcin kawance tsakanin Sin da Serbia, da aiwatar da kyawawan matakai da za su amfani al’ummun sassan biyu, da ingiza zaman lafiya da ci gaban duniya, da hada gwiwa wajen gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama.

Shugaba Xi Jinping ya kara da cewa “Bai kamata mu manta da yadda shekaru 25 da suka gabata, dakarun tawagar NATO suka jefa bam a ofishin jakadancin Sin dake Yugoslavia ba. Al’ummun Sin na martaba zaman lafiya, amma ba za su bari mummunan abu da ya faru a tarihi ya sake maimaituwa ba. Kawance na jini da tsoka tsakanin Sinawa da al’ummar Serbia, ya zamo abu da a kullum sassan biyu ke tunawa da shi, wanda kuma zai ingiza sassan biyu wajen tunkarar ci gaban su tare. A shirye muke mu yi aiki tare da abokanmu na Serbia, wajen nacewa burikan mu na asali bisa gaskiya, kana za mu ci gaba tare, za mu bude sabon babin bunkasawa, da kara farfado da kasashen mu, da gina al’ummar Sin da Serbia mai makomar bai daya a sabon zamani. (Mai Fassarawa: Saminu Alhassan).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SerbiaXi JinpingZiyarar Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Irin Hikima Da Karfin Da Suka Ba Da Muhimmin Tasiri

Next Post

Matashiya Ta Kashe Kanta Ta Hanyar Shan Maganin Ƙwari A Delta

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

11 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

12 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

13 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

14 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

15 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

16 hours ago
Next Post
Matashiya Ta Kashe Kanta Ta Hanyar Shan Maganin Ƙwari A Delta

Matashiya Ta Kashe Kanta Ta Hanyar Shan Maganin Ƙwari A Delta

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.