• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Turai Zai Yaukaka Daidaiton Dangantaka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwar Sin Da Turai Zai Yaukaka Daidaiton Dangantaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke gudanarwa a kasashen Faransa, da Serbia, da Hungary, ta kasance muhimmin matakin yaukaka dangantakar diflomasiyyar bangarorin biyu.

Kasar Sin da kasashen Turai karkashin jagorancin kungiyar EU, muhimman bangarori ne biyu dake ingiza manufar samar da tasirin fada-a-ji daga bangarori daban daban, kuma sassan biyu na matukar goyon bayan dunkulewar duniya, a bangare daya kuma, sun kasance bangarori masu rungumar mabanbantan wayewar kai a duniya. Don hake ne ma masharhanta da dama ke kallon alakar Sin da Turai a matsayin mai da matukar muhimmanci wajen saita akalar ci gaban duniya baki daya.

  • An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary
  • Shugaba Xi: Har Kullum Sin Da Hungary Na Kallon Alakarsu Daga Mahanga Mai Fadi Da Wa’adi Mai Tsawo

Masu fashin baki na ganin cewa, Sin da kasashen tarayyar Turai ba su da manyan banbance-banbancen neman cimma moriya, ko sabani ta fuskar siyasar yankunan su. Kaza lika, batutuwan da suke dunkule sassan biyu wuri guda, sun rinjayi banbance-banbancensu. Hakan ne kuma ya sa har kullum suke ta kokarin yaukaka alakar su, ta yadda za su ci gaba da kasancewa sahihan kawaye abun koyi, su kuma ci gaba da yin hadin gwiwa, da cimma moriya tare a yanzu da ma nan gaba.

A bangarenta, a ko da yaushe kasar Sin na daukar tarayyar Turai a matsayin muhimmin karfi dake da tasiri a harkokin kasa da kasa, tana kuma sanya batun raya dangantakarta da EU a sahun gaba cikin harkokin diflomasiyyarta.

Bisa hakan ne ma a bazarar shekarar 2014, shugaba Xi ya ziyarci helkwatar kungiyar EU, inda a lokacin ya gabatar da shawarar hada karfi da karfe tsakanin kasarsa da EU, a fannonin wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da gudanar da sauye-sauye, da bunkasa wayewar kai. Har yanzu kuma wannan kuduri bai sauya ba, yana kuma ci gaba da zama alkiblar raya dangantakar sassan biyu a halin da ake ciki yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Yayin da duniya ke kara tsunduma cikin hali na rashin tabbas, da rigingimu nan da can, yana da kyau Sin da EU su wanzar da tattaunawa ta kut da kut, su kuma mayar da hankali ga hadin gwiwar cimma moriyar juna, daga fannin ingiza ci gaban bangarorin biyu zuwa tunkarar kalubalolin dake addabar duniya baki daya.

Tabbatattun shaidu sun nuna cewa, muddin Sin da EU sun yi aiki tare wajen saita alkiblar da za su bi domin bunkasa kan su, ko shakka babu hakan zai iya kai su ga cimma burikan da suka sanya gaba, tare da haifarwa alummun su da tarin alherai.

A halin da ake ciki, Sin na kan gaba a jerin sassa mafiya muhimmanci ga Turai a fannin hada-hadar cinikayya. Duk da tafiyar hawainiya da tattalin arzikin duniya ke yi a yanzu, a shekarar bara, jimillar darajar cinikayya tsakanin Sin da EU ta kai dala biliyan 783. Kaza lika Sin na yiwa Turai maraba a fannonin cin gajiyar hadin gwiwar kasuwanci, da raya kimiyya da fasaha, da bunkasa hidimomin sarrafa hajojin masanaantu da rarraba su ga sassan duniya, ta yadda sassan biyu za su ci gajiyar bai daya, da samun nasara da walwala tare.

Ko shakka babu sannu a hankali, hadin gwiwar Sin da Turai na bunkasa, musamman ma a fannonin da duniya ke mayar da hankali yanzu a kansu, kamar tattalin arziki na dijital, da bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da cin gajiya daga sabbin makamashi, da kirkirarriyar basira.

Bunkasar Sin wata dama ce ga EU, kana daidaita kawancen sassan biyu zai taimaka matuka wajen shawo kan kalubale da EU ke fuskanta. A halin da ake ciki, karin sassan Turai na dada fahimtar muhimmancin hada gwiwa da Sin, wajen magance matsalolin makamashi, da hauhawar farashin hajoji da EU ke fuskanta, a daya bangaren dangantakar sassan biyu za ta kyautata takara mai tsafta tsakaninsu, da haifar da gajiya ga Sin da turai da ma duniya baki daya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaEUHungaryTarayyar Turai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwastam ta Mika Jabun Dalar Amurka Da Jirage Marasa Matuka 148 Da Ta Kwace Ga EFCC Da Sojoji

Next Post

Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

Related

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

2 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

3 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

22 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

23 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

24 hours ago
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

1 day ago
Next Post
Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

LABARAI MASU NASABA

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana ƘoÆ™arin Ganin Ƙarshen HaÆ™urin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana ƘoÆ™arin Ganin Ƙarshen HaÆ™urin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.