• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya biya tsofaffin ma’aikatan jihar bashin haƙƙoƙin su na barin aiki, wato Garatuti, wanda suka biyo tun na shekarar 2011, kuɗaɗen da suka haura Naira Biliyan 4.

Ma’aikatan jiha da na Ƙananan Hukumomin jihar da su ka bar aiki, ba su samu haƙƙoƙin su ba na tsawon waɗannan shekaru, an tantance su an biya su.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa an biya tsofaffin ma’aikatan jihar da na Ƙananan Hukumomi waɗannan kuɗaɗe bayan tantance sahihancin su.

Ya ce, gwamnatin jihar Zamfara ta biya tsabar kuɗin da ya kai ma Naira Biliyan 4,337,087,492.06 a rukunoni huɗu na tsofaffi ma’aikatan.

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ce, “A watan Faburairu, Gwamna Dauda Lawal ya kafa wani Kwamiti, wanda aka ɗora ma alhakin tantancewa tare da biyan tsofaffin ma’aikatan da suka bar aiki tun shekarar 2011, a ƙoƙarin sa na gyara tsarin aikin gwamnati a jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

 

“Bayan kammala wannan tantancewar, sai ta bayyanar wa gwamnati cewa ana bin jiha da Ƙananan Hukumomi Naira Biyan 13.4.

“A biyan rukuni na farko, na biyu da na uku, an biya mutum 1,088 da aka tantance dukkan haƙƙoƙin su, inda aka biya N1,836,836,018.95

“A wannan watan, an biya mutum 284 da aka tantance kuɗaɗen su, wanda ya kai ma N499,435,942.42 a rukuni na huɗu. Hukumar Fansho ta jiha ta biya kuɗaɗen da suka kai ma N2,336,271,961.37.

“Bugu da ƙari, akwai ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman Firamare su kimanin 1,744, waɗanda suka bar aiki a tsakanin shekarun 2011 da 2018, kuma tuni an biya su haƙƙoƙin su da ya kai ma Naira Biliyan N2,000,815,530.69 a rukuni huɗu.

“Wannan biyan bashin kuɗin barin aiki, ba ƙaramin gagarumin ci gaba ba ne a wannan gwamnatin, wanda kuma babu makawa, zai kawo sauƙi ga rayuwar waɗanda suka amfana, bayan jiran tsammani na shekaru masu yawa.

“Gwamnatin Dauda Lawal ta nuna aniyar ta na jajircewa wajen cika alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiDauda LawalGwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

18 minutes ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

2 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

7 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

8 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

9 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

12 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.