• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Dokar Barci…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mai Dokar Barci…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alamun kasashen da suke ikirarin kare hakkin bil-Adama, su ne kuma suke take wannan hakki ta hanyar kashe fararen hula, wadanda ba su san hawa ba balle sauka. Wai mai dokar barci ya bige da gyangyadi.

Sanin kowa ne cewa, a kan tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa wasu kasashe dake fama da rikici ko tashe-tashen hankula ne, domin su tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin wadannan kasashe, amma sabanin haka, sai irin wadannan kasashe, har ma gasar kashe fararen hula suka yi a kasar Afghanistan.

  • Dan Ta’addar Da Aka Nada Sarauta A Zamfara Ya Kashe Mutum 100 A Katsina – ‘Yansanda

Wani binciken da kafar yada labaran BBC ta gudanar kan shaidun da suka hada da rahotannin sojojin Birtaniyya, da sakonnin imel, da hotunan ramukan harsashi a wurin, ya nuna cewa, wasu mambobin tsohon rukunin mai ba da hidima ga soja na musamman na Birtaniya dake Afghanistan, sun sha kashe fursunoni da fararen hula da ba sa dauke da makamai, har ma su kan yi gasar kisan mutane, daga cikinsu, akwai yiwuwar wata runduna ta kashe mutane har 54 ba bisa kai’da ba, a wa’adinsu na watanni 6 a wurin.

Bayan fallasa wadannan laifuffuka, ma’aikatar tsaron Burtaniya, ba wai kawai ta ki neman afuwa, ko daukar alhakin kai harin ba, amma sai ta yi kokarin yin rufa-rufa, tana mai zargin rahoton na BBC da cewa wai “labarai ne da ba su dace ba kuma wai ba daidai ba ne”. Wannan shi ne kora kunya da hauka.

Hasali ma, ba sojojin Birtaniya ne kawai suka kashe fararen hula babu gaira babu dalili ba. A watan Disamba na shekarar 2020, ma’aikatar tsaron kasar Austriliya, ta fitar da rahoton bincike game da kyamar bil-Adama da sojojinta suka yiwa fararen hula a kasar Afghanistan.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A bangaren Amurka, wadda ke zama kanwa uwar gani, mamayar da aka yi a kasar Afghanistan na tsawon shekaru 20, ta yi sanadiyar rayukan ’yan kasar dubu 174, ciki har da fararen hula dubu 30. Wadannan kasashe su ne suke ikirari kare hakkin Bil Adama a ko da yaushe, to yaya za su bayyana kisan gillar da suke yiwa mutanen da ba su san hawa ba balle sauka a kasashen waje?Duniya na bukatar amsa daga gare su.

Sanin kowa ne cewa, yarjejeniyar Geneva ta bayyana karara cewa, ba daidai ba ne kisa, ko tilastawa, ko musgunawa da ma korar wadanda ke zaune lafiya, yin hakan ta ce haramun ne a lokacin yaki, kuma wadanda ba su taka rawa a yakin ba, za a mutunta su a kowane hali.

Kasashen Amurka da Birtaniya da Austriliya, dukkansu sun sa hannu kan wannan yarjejeniya, amma kuma sun rufe idanunsu, suka kuma rika keta dokokin kasa da kasa, da ma harkokinsu da suka shafi dan-Adam.

Baya ga yadda suke kashe mutanen da ba su ji ba su gani ba. Laifukan da suke aikatawa, laifi ne ga daukacin bil-Adam, don haka sun cancanci a yi musu adalci. Dole ne kasashen duniya su yi adalci ga wadanda ba su ji ba su gani ba. Domin babu ran da ya fi wani. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Next Post

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

1 hour ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

1 hour ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

3 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

6 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

8 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.