• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon makon nan, fadar White House ta Amurka, ta sanar da sabbin matakan kariyar cinikayya kan kamfanonin fasahohi masu tsafta na kasar Sin, ciki har da ninninka harajin ababen hawa kirar kasar Sin masu aiki da lantarki da ake shigarwa Amurka zuwa kaso 100 bisa dari.

Ko shakka babu, wannan mataki ne da ya fi kama da farfagandar siyasa, duba da cewa an dauke shi ne a cikin shekarar babban zaben kasar, ko alama bai yi kama da mataki mai la’akari da tsarin kyautata tattalin arziki ba.

  • Shugabannin Sin Da Rasha Sun Tattauna Da Juna
  • Kasar Sin Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Karin Haraji Da Amurka Ta Yi

Masharhanta da dama na cewa, harajin baya ma da Amurka ta kara kan irin wadannan kayayyaki zuwa kaso 25 bisa dari, ya riga ya kore irin wadannan nau’o’in motoci daga shiga Amurka. To amma da karin na baya, da wanda aka sanar a ’yan kwanakin nan, ba abun da za su haifar sai koma baya ga Amurka a fannoni da dama, kuma ko kadan wannan mataki na kokarin dakile ci gaban sashen makamashi mai tsafta na Sin, ba zai taimakawa Amurka ta bunkasa nata masana’antun fannin ba.

Da farko dai, matakan za su hana Amurkawa cin gajiya daga ababen hawa masu rahusa, masu amfani da tsaftacaccen makamashi. Kaza lika hakan zai hana su amfana daga takarar kasuwa, tare da tursasa su sayen ababen hawa masu matukar tsada.

Ko da a bangaren masana’antun sarrafa karafa ma, a shekarun baya bayan nan, matakan da Amurka ta rika dauka na kariyar cinikayya, ba su taimakawa kasar da komai ba, matakan ba su dakile raguwar guraben ayyukan yi ba. Maimakon haka, sai ma kara tsadar hajojin kamfanonin fannin suka haifar, da takaita kyakkyawar takara ga kamfanonin na Amurka, daga karshe hakan ya illata tattalin arzikin kasar.

Labarai Masu Nasaba

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Manazarta dai na ganin maimakon kakkaba shingen cinikayya, kamata ya yi ’yan siyasar Amurka su amince da muhimmancin rungumar takara mai tsafta, su karfafa gwiwar kirkire-kirkire da bude kasuwanni, ta yadda takara za ta kai ga samar da sauki, da bunkasar tattalin arzikin dukkanin sassa, idan kuma ba haka ba “Kaikayi zai koma kan mashekiya”. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fasahar kere-kereKimiyyaWTO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara

Related

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

49 minutes ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

1 hour ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

18 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

18 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

20 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

23 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Amurka

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.