• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani sakamakon bincike na jin raayin alumma, da jaridar The Guardian ta Amurka ta wallafa a baya bayan nan, ya nuna yadda duk cikin Amurkawa biyar, daya daga cikinsu ke ganin abu ne mai kyau, a cimma burin siyasa ta hanyar tarzoma.

Ko shakka babu hakan abun tsoro ne, da tayar da hankali, ganin cewa wannan tunani ya yi hannun riga da ainihin tushen dimokaradiyya, wanda ya tanadi cimma duk wani buri ta maslaha da kwanciyar hankali.

  • Sin Ta Mayar Da Martani Ga Rahoton Shekara-shekara Na Fataucin Bil Adama Na Amurka

Wani abun lura game da wannan bincike, shi ne yadda Amurkawa ke saurin yarda da farfagandar ’yan siyasa, wadda ke haifar da rashin yarda, da nuna kyama, da amincewa daukar matakan tada zaune tsaye, yayin da suke son cimma wani buri na siyasa ko zamantakewa.

Ko da yake dai Bahaushe kan ce Barewa ba za ta yi gudu dan ta ya yi rarrafe ba. Duniya ta ga misalin irin wannan tunani tun daga kan jagororin Amurka, inda alal misali, a ranar 6 ga watan Janairun shekarar bara, daruruwan magoya bayan tsohon shugaban kasar Donald Trump, suka yi kutse cikin ginin majalissar dokokin kasar na Capitol, da nufin hana bayyana tsohon shugaban kasar a matsayin wanda ya sha kaye a babban zaben da ya gabata.

Wanda hakan ya sabbaba rasuwar mutane 7 da jikkatar gwamman mutane. Masu bibiyar lamarin sun tabbatar da cewa shi kansa tsohon shugaba Trump, ya nuna wasu alamu na goyon bayan wancan kutse.

Labarai Masu Nasaba

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Masharhanta dai na ganin idan har wannan yanayi na yin watsi da tushen dimokaradiyya ya ci gaba da kamari a Amurka, mai yiwuwa kasar ta fuskanci manyan bore masu nasaba da siyasa a nan da ’yan shekaru masu zuwa.

Domin kaucewa hakan, wajibi ne jagororin kasar su yi karatun ta-nutsu, su yi hangen nesa wajen wayar da kan Amurkawa, game da illar dake tattare da daukar doka a hannu, da kin amincewa da mabanbantan raayoyi, da nuna isa, wadanda dukkaninsu munanan dabiu ne da ka iya haifarwa kasar da maras ido.

Uwa uba kuma, ya zama wajibi gwamnatin Amurka ta dawo daga rakiyar manufarta ta shiga sharo ba shanu, da nuna karfin tuwo ga sauran kasashe, ko nuna kyama ga hanyoyin ci gaba da sauran kasashe suka zabawa kan su, domin kuwa irin wannan tunani ne ke haifarwa ’yan kasar ta yanayi na kangarewa, da kin karbar gaskiya!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ba Za Ta Iya Bata Sunan Xinjiang Ba

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Related

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

2 hours ago
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

3 hours ago
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

4 hours ago
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
Daga Birnin Sin

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

5 hours ago
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

6 hours ago
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
Daga Birnin Sin

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

7 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.